Tuesday 23 May 2017

AKAN SO 50


*💘💖AKAN SO💖💘*

~Written by~ :Luβπα Sufyαπ

www.Loobnerh.blogspot.com

Wattpad: LubnaSufyan

          50

*EPILOGUE*

*Tabbas zan kewar characters din dake cikin AS gabaki dayansu. Sai dai ina jin dadin yanda suka taba rayuwata ta fanni da dama. Da kuma yanda suka taba rayuwar readers din*

*Abu uku daga Luβπα Sufyαπ zuwa ga dubban mutanen dake nuna mata kauna*

*1. Rayuwa makaranta ce mai fadin gaske. Zata hadaka da mutane kala kala. Zata tabaka ta inda baka zato. Ta wani fannin farin ciki. Ta wani fannin akasin hakan. Ka riqe ALLAH a komai*

*2. Kaddara. Banda kalaman da zan amfani dasu wajen kokarin fassarata. Saboda haka zance duk kalar daka tsinci kanka a ciki. Abu biyune mafita. Ka karbeta sanin kana daga cikin masu kusanci da Ubangiji. Mummuna ko mai kyau. Ka riqe ALLAH a komai*

*3.Zumunci da hakuri. Abubuwane da suke gogayya da juna a lokacin da rayuwa ta tabaka ta rukuni da dama. Karka duba kalar kaunar yan uwanka a gareka. Ba wannan bane mai muhimmanci. Ka duba girman kaunarka a garesu. Ka riqe ALLAH a komai. Zai kasance dakai a komai*

*Nagode. AnaTare. Like sosai AnaTare. Like seriously AnaTare. Irin totally AnaTare*

"I feel ridiculous cikin kayan nan wallahi"

Dakuna fuska safiyya tayi tana balle mishi maballin rigar. Ta kalle shi sosai. Kalar shaddar ruwan kasa ne mai haske sai yai shige da idanuwanshi.

"Kaga yanda kai kyau"

Damqe fuska yai yana jin gabaki daya manyan kayan sun takuranshi. Duk ya shake.

"Nikam dakin barni nasa riga da wando abuna"

Daure fuska safiyya tayi.

"Ka kalli luku da mimi sun girma. Ko affa (Mai sunan baban safiyya) ya girma. Yaushe zaka fara saka manyan kaya.

Oya muje"

Fuska a daqune da alamar takura ya fita falon. Mimi ce a zaune da litattafan islamiya baje a kasa tana assignment.

Jin tafiya yasa ta dago. Sauke idanuwanta tai kan fu.ad lokaci daya ta yamutsa fuska.

Kallonta safiyya tayi. Gaba daya expressions din nan irin na fu.ad ne. Duk ya koya mata.

"Menene wannan kasa dady?"

Ta tambaya fuska a yatsine. Hararta safiyya tayi. Fu.ad ya kalli safiyya dake fassara 'Bana gaya miki ba'.

"Kaya sunan su. Manyan kaya"

Safiyya ta amsa ma mimi.

"You look different"

Mimi ta fadi tana maida kanta wajen assignment din da take. Karasawa fu.ad yayi bai damu da zaman dayai a kasa zai squeezing mishi kyanshi ba.

"Daban in a good or bad way?"

Ya bukata. Dagowa mimi tayi tadan murmushi ta rausayar da kanta gefe alamar tana tunani.

Dakuna mata fuska fu.ad yayi. Hakan ya bata dariya.

"Kana sakawa ko yaushe. In a good way"

Murmushi yayi.

"Kome queen take so"

Ware idanuwa safiyya tayi.

"Tunda yar ka tace kayi kyau ka yarda. Ni da na fada ai baka dauka ba"

Kallonta Mimi tayi da smug face.

"Yafi sona ko dady?"

Tsare shi da idanuwa safiyya tayi. Yadan ware mata idanuwa. Mikewa yai daga kusa da mimi ya taka inda take.

Idanuwanshi ya sauke cikin nata. Godiyarshi da kaunarta yake nuna mata. Yake son tabbatar mata. A shekaru goman nan rayuwa ta musu wani irin sauyi naban mamaki.

Allah ya musu kyauta yara har biyu bayan mimi dukkansu maza. Yanayin kallon da yake mata ya kashe mata jiki.

"Ina sonki sosai"

Ya fadi kasa kasa. Dakuna mishi fuska tayi alamar Mimi na falon. Dan juyawa yayi yaga bama ta su Mimi take ba.

Rankwafawa yai. Tai saurin matsawa. Da sauri ta juya tai bedroom dinsu. Yabi bayanta. Yana shiga tasa hannuwanta jikin wuyanshi.

"Kai ko"

Tarin wasa ya fara. A dole ta shaqe shi. Sauke hannayenta tai tana dariya.

"Ka bata mun yarinya. Duk irin abinka ta dauka"

Cute face yai mata.

"Like daughter like dady"

Murmushi safiyya tayi. Tana kai hannu tare da ja mishi hanci.

"Allah ya rayamun ku"

"Amin. Tare dake ma"

Ya fadi yana janyota jikinshi. Sumba ya manna mata mai taushi a lips.

"Alhamdulillah da kyautar iyalai irinku"

Ta amsa da.

"Alhamdulillah da kaddara irin tamu"

Lumshe idanuwanshi yayi. Yana hugging dinta jikinshi.

"Ina tunanin me Nana zata ce ne da zata ganni da wannan kayan"

Dariya safiyya tayi. Cikin kwaikwayon muryar Nana tace.

"Dady me mumy ta baka kasa haka?"

Sosai yake dariya da dukkan zuciyarshi. Yanajin dadin yanda har yau memories din Nana na saka su farin ciki irin wannan.

Ta wani fannin yana jinjina ma rayuwa. Yana kara ganin yanda take tamkar makaranta. Kowa da yanda zai fahimci tashi.............!!!

Nikuma anan nake muku sallama. Da fatan alkhairi a rayuwa gabaki daya.

*ALHAMDULILLAH*

*Aliyu tsagem. Fahad. Ayna.u mardiyya. Ummie jafar. Yusra abdu fari. Biebie Isa. ALLAH YA SADAKU DA ALKHAIRI A DUK INDA KUKE*

*Whatsapp*

Daukacin wa.annan groups din

- Taskar novels.
- Taskar Lubabatu maitafsir
-Taskira
-Ummie jafar novels
-Billy galadanchi novels
-Da sauran da ba zasu lissafu ba.

*Ina godiya da karamcinku. Ina muku fatan alkhairi a duk inda kuke*

*WATTPAD*

*Bazan taba iya lissafo gabaki daya sunayenku ba. Ku sani. Wallahi dukkan comments dinku yana da muhimmanci gaske a wajena. Dukkan kwarin gwiwarku yana da tasiri a rayuwata data rubutuna gabaki daya. Kaunata a gareku mai girma ce*

*Architect ishaq (Bifham) fatana a gareka guda dayane. (Ka zama cikin nutsuwa da kwanciyar hankali)

*YAYA. (Kana nan a bakin ciki da farin ciki. Kana nan sanda na rasa hope akan komai. Kana nan a ko ina. Ina fatan Allah ya kasance dakai a ko ina na rayuwarka)

*Allah ya hadamu a aljanna*

*Ina neman gafarar duk wanda na batama. Na yafe ma kowa. Laifin dayaimun a bisa sani ko rashin sani. Allah ya yafe mana gabaki dayanmu. Amin amin*

*AnaTare*

*ALLAH YA NUNA MANA RAMADAN LAFIYA* (Amin thumma amin)

No comments:

Post a Comment