Tuesday 23 May 2017

AKAN SO 48

*💘💖AKAN SO💖💘*

~Written by~ :Luβπα Sufyαπ

www.Loobnerh.blogspot.com

Wattpad: LubnaSufyan

                48

*A ko da yaushe a rayuwa idan kace zaka dinga duba baya. To da wahalar gaske gaban tai maka dai dai*

*Bazai rageka da komai ba dan ka yafe. Ba ace ka manta ba. Wannan abune mai wahala. Baiwa ce da bakowa Allah yaiwa ba*

*Sai dai ka sani ana ci gaba da zama da juna ne bawai dan an manta bacin ran daya faru ba. Ana zama ne saboda an YAFE*

*Allah ya nuna mana RAMADAN lafiya. Amin thumma amin*

*Ba saina ce nagode da comments dinku da prayers ba saboda ai #AnaTare. Like sosai sosai*

*TWO MORE pages In shaa Allah*

Yana shigowa gidan da sallama yaga baiga nuriyya ba. Ciki ya shiga ya duba bedroom dinta.

Dan yasan bata cika zama falo ba. Tafi gane tai kwance a bedroom din in bashi ya dawo yazo ya fito da ita ba.

Zuciyarshi yaji tana dokawa babu dalili. A rikice ya fito yana fadin.

"Nuriyyaaaa"

Da saurinta ta fito daga cikin. Idanuwanta ta sauke cikin nashi. Wata ajiyar zuciya ya sauke yana tura hannunshi daya cikin sumar kanshi.

Da mamakin ganin tsoron da har lokacin bai barshi ba yasata fadin.

"Yaya farhan. Lafiya dai ko?"

Kai ya daga mata yana dora murmushi a fuskarshi.

"Ina kitchen ne banji shigowarka ba"

Ta fadi a sanyaye hadi da dorawa da.

"Ka daina tunanin zaka nemeni ka rasa yaya farhan. You are the only family da nake da.

Please banajin dadi"

Kunyarta yaji ta rufe shi. Har ranshi yana tsoron ya nemeta ya rasa. A yanzun shima bashida wani family bayan ita.

"Na daina. I am sorry"

Kai ta daga mishi alamar komai ya wuce.

"Nace ki daina damuwa da dafa abinci. Zamu iya fita waje muci"

Dan murmushi tayi mishi tana jin wani quna a zuciyarta. Nawaf ya koya mata kyamar abincin waje komin tsaftar restaurant ko hotel kuwa.

"Ba wani aiki bane. Tunda babu yawa"

Kai ya daga mata ya zagaya ya zauna kan kujerar.

"Zo mu zauna"

"Barin sauke girki sai inzo"

Ta fadi tana juyawa. Bata fi mintina goma ba ta fito. Waje ya samu gefenshi ta zauna.

Kallonta yai sosai. Muryarshi da fuskarshi tana nuna mata muhimmancin maganar da yake son fada.

"Naje gidan anty ne yau. Naje inji ko tana da wani abu da ya rage na lokacin data tsince ki.

So ba a samu komai ba sai School back dinki. Na karbo amman ban bude ba. Banma san yanda zakiyi handling abin ba na bari in fara fada miki"

Kan nuriyya a kasa tana jin hawayen da suka taru a idanuwanta suna zuba. Zuciyarta dokawa take.

"Nuriyya....."

Ya kira a hankali. Tun a hanya yake tababar fada mata. Yadan samu a satin nan ta fara warwarewa har tana dan hira dashi.

Zai jagula komai akan maganar da babu tabbas a cikinta. Babu ma wani hope ko za.a samu wani clue cikin jakar.

Hannunta takai ta kamo na farhan ta dumtse. Karo na biyu da jikinsu ya hadu tun zuwanta gidan. Kaman yanda yai mata alkawarin zama duk abinda take son shi ya zame mata har saita shirya canzuwar hakan.

Bai karya ba. Beside inya kula bata son magana bata waje yake.

"Ina tsoron a bude jakar da kace ka karbo a samu babu komai a ciki. Ina tsoron ko bazan taba ganin dangina ba.

Idan ina dasu kenan. Bansan me ya kamata inyi ba"

Dayan hannunshi yasa ya hade nata cikin nashi duka biyun. Cikin idanuwa yake kallonta. Sannan yace.

"Rashin budewa a duba zai sa ki zama cikin tambaya a ko da yaushe.

Budewar bazai cutar dake ba nuriyya.  Kilanma ki tuna wani abu. Allah kadai yasan me ya boye miki a bayyanar gaskiyar nan.

Inkuma kina so magana da anty ne directly sai muje"

Da sauri ta girgiza mishi kai. Wani irin tsoro na shigarta. In akwai abinda tafi tsana bai wuce ta sake dora fuskarta kan azzalumar mata kaman anty ba.

Ko a mafarki bata fatan Allah ya sake hadasu ballantana kuma idanuwa biyu.

"Bana son sake ganinta yaya farhan. Na tsaneta wallahi"

"I understand...."

Da rauni a muryarta tace.

"Zamu bude jakar tare. In babu kai bazan iya ba"

Kasa controlling emotions dinshi yayi. Ya kara matsawa ya sumbace ta a kunci sannan ya saki hannunta ya mike yana ficewa daga falon.

Hannu tasa ta goge fuskarta. Zuciyarta na wani irin dokawa. Tana jin ya shigo da sauri ta daga kai ta kalle shi.

Kamun ta maida kallon kan yar jakar dake hannunshi. Kurar da jakar tayi ya hana asalin kalarta ta fito. Kaman ash colour. Kara sowa yayi ya zauna.

Sannan ya mika mata jakar ta karba tana jujjuyata. Da duk wani abu na jikinta take son taji wani connection tsakaninta da jakar ko ta tuna wani abu ko ya yake amman ta kasa.

Muryarta na rawa tace.

"Na kasa tuna komai yaya farhan"

Dafa hannunta yayi. Ya na karbar jakar ya ajiye kan kujera.

"May be shekarunki ba masu yawa bane da zaki rike wani abu. Ki bude"

Kai ga daga mishi. Zuciyarta na wani irin dokawa. Ji take kaman inta bude jakar zata iya ganin wani abu dazai tuna mata asalinta.

Ta wani fannin kuma tanajin tsoron yanda ta daga burinta har haka. Jin farhan ya sake dafa hannunta ya sata jan wani numfashi sannan ta sa hannu kan zip din jakar ta bude.

Bugun zuciyarta na karuwa. Hannu tasa ta daga jakar hadi da zazzageta kan kujerar. Tasa hannu tana taba kayyakin da suka zubo daga ciki kaman zasu bata amsar data kasa samu.

Books ne a ciki gabaki daya na yan Nursery 1. Farhan ne yasa hannu ya dauki guda daya daga ciki. Yaga inda anty taga asalin sunan Nuriyya kenan.

Gashi nan da manyan baki a rubuce. 'Nuriyya habeeb danori'. Habeeb danori farhan yake maimaitawa cikin kanshi yana tunanin inda ya taba jin sunan.

Sosai yake dubawa. Dan ware idanuwa yai ya kalli nuriyya da idanuwanta ke kafe kan littatafan da take ta shafawa.

Ya bude baki sai ya fasa. Gidan mai ne yagani wajen bachirawa. Sai dai zai iya yiwa habeeb danori da yawa cikin garin kano.

Baya son ya daga mata burinta sai ya tabbatar tukunna. Duk da yana da wani irin feeling mai karfi kan hakan. Bazai daga mata buri yazo ya tarwatsa shi ba.

Yana kallonta ta dauki littafi daya tana sa hannu tana shafa wajen da sunan yake.

"Asalin sunana Nuriyya. Anty tagani. Taga sunana ta kasa kaini inda dangina zasu nemeni.

Saboda me? Meye ribarta na tsintata ta kasa kaini inda za a ganni? Amfanin me nai mata?"

Shiru farhan yayi saboda baisan me ya kamata yai mata ba. Matsawa yayi ya kama Hannuwanta. Kwacewa tayi.

"Saboda me? Ina da family kaima kagani. Kaga shaida yaya farhan me yasa zata tarwatsa mun rayuwa?

Duk shekarun na ina tunanin ko kalar mahaifina bazan taba sani ba. Ina tunanin mahaifiyata karuwa ce.

Kasan tashin hankalin dake cikin hakan?"

"Nuriyya please calm down....."

Farhan ya fadi. Cikin hargowa tace.

"No yaya farhan. Ba zaka taba ganewa ba saboda kayi normal rayuwa ba irin tawa ba"

Kallonta yake maganganun data fada suna masa wani irin zafi. Muryarshi can kasa yace.

"Nuriyya. Ki bar maganar nan. Zan nemo miki su in shaa Allah"

Hawayen da suke zuba idanuwanta tasa hannu ta goge.

"Idan kuma ba sa nan fa? Ba zaka taba ganewa ba"

A tsawace yace.

"Yes bazan gane ba nuriyya. Na dauka kinsan kadan daga cikin rayuwata.

Kinsan waye babana. Bance yafi anty ba. Ban kuma ce kalar su daya ba. Ki kalle ni sosai.

Na miki kama da wanda yai rayuwa normal?"

Shiru tayi tana kallonshi yanda ya birkice lokaci daya.

"Ko kin taba tambayata ina kanwata da nake baki labari?

No baki tambaya ba. Ni kuma ban fada miki ba saboda what is there to tell?

Ince nuriyya kinsan me ya faru da farhana kuwa? Ina kallo babana ya sha giya ya bugu yace saita bishi sun fita unguwa.

Ina tsaye saboda tace tana son zuwa gudunma tashin hankalin shi nabarta.

Bayan komai na jikina na mun ihun kuskuren hakan. Ina kallo yaja mota suka bar cikin gida ban tsayar dasu ba.

Yeah naga kuskurena awa biyu tsakani da aka jeramun gawarsu a gabana.

Sai dai kinsan me? I deserve the pain na mutuwar farhana saboda ni ne sila. Him? That Monster? I wish baiyi mutuwa mai sauki ba......"

Inalillahi wa ina ilaihi raji.un kawai nuriyya ke fadi cikin zuciyarta. Sai yanzun taji dalilin da duk murmushin da farhan zai akwai wani irin sadness a karkashi shi.

Hannu tasa ta dafa mishi cinya. Amman kaman ma baya jinta.

"Yaya farhan....."

Ta fadi hawaye na zubo mata ganin yanda jikinshi ke kyarma. Yanda komai nashi ya canza. Yanayin ciwon abinda yake ji bayyane a fuskarshi.

Juyowa yai ya kalleta sosai.

"I don't know exactly yanda kike ji. But bake kadai kike hurting ba. Bake kadai bace nuriyya"

Mikewa tai ta matsa ta zauna kan cinyarshi. Kamun yagama mamaki tayi hugging dinshi sosai. Kuka take. Shikam ya kasa. Yanajin kalar raunukan da yake dasu zafinsu da ciwonsu ya girmi hawaye.

Riketa yai a jikinshi yana jin yanda yanayin ke fifita mishi inda yake masa zafi. Sumba ya manna mata a gefen fuska.

"Ki daina kuka. In shaa Allah zan nemo miki family dinki. Za.a gansu"

Kai take dagawa tana sake kankame shi. Cikin kunnenshi tace.

"Kaima ka gano naka please. Ka gano mana family dinmu"

Shiru yayi yana juya maganarta.

"No naki dai nuriyya. Mum na bata da kowa. Shikuma....... Yeah sunyi gefe lokacin da yake abusing dinmu.

Saboda yana da kudi babu wanda zai iya mishi magana"

Sake rike shi tayi.

"Nasani. Ka yafe musu dukkanmu muna kuskure a rayuwarmu"

Lumshe idanuwa farhan yayi.

"Mu bar maganar for now please"

Dagowa tai daga jikinshi. Ta kalli fuskarshi sosai.

"For now"

Ya daga mata kai da yake nuna alkawarin zasu sake maganar amman ba yau din ba. Komawa tai jikinshi ta kwanta luf.

Ya riketa yana lumshe idanuwanshi. Rayuwa makaranta.....!

"Na dauka sai da yamma zamu tafi"

Safiyya ta fadi a sanyaye tana kallon fu.ad. Girgiza mata kai yayi.

"Mu koma gida kawai. Zama anan bazai sake komai ba."

Kai ta daga mishi ta na dauke idanuwanta daga fuskarshi. Tana jin ciwon yanda zata koma gidan su da yake cike da memories din nana.

Yau kwana hudu kenan da rasuwar. Su dukansu kallo daya zakai musu ka fahimci yanda rayuwa ta koya musu darasi da dama.

Musamman safiyya da fu.ad da sukai wata irin rama. Ya karanci me take gudu tsaf. Ya share ne saboda yasan gudu wa feelings dinsu bazai canza komai ba.

Da yawan gudun da suke da yawan yanda zai musu zafi idan ya kamo su. Ya riga da ya fada ma momma zasu koma gida tun dazun.

Itama da taga kaman yayi sauri dayai mata bayani saita fahimta.

"Bara to in dauko mayafina sai in sallama da momma"

Kai kawai fu.ad ya iya daga mata. Baiko zauna ba dan yasan ba dadewa zatai ba.

Shi kanshi zuciyarshi cike take da tsoron kalar ciwon da zaiji in suka karasa gidan. Kewar Nana har cikin tsokarshi yake jinta.

A zuciyarshi wani irin fili ne tabari da babu wanda zai iya maye shi. Wajenta ne ita kadai. Lumshe idanuwanshi yai hannuwanshi cikin aljihu.

Murmushinta ya tuna da yanda take bude idanuwanta idan taganshi. Baisan sanda murmushi ya kwace mishi ba. Cikin zuciyarshi yake fadin.

"Allah ya haskaka kabarinki nana. Kin barmu da kewa ko? Nagode da tare da kewarki akwai moments irin wa.annan"

Tabashi yaji anyi. Da sauri ya bude idanuwanshi ya sauke su cikin na safiyya. Lokaci daya murmushin dake fuskarshi ya bace.

"Murmushin me kake?"

Hannunta ya kama suka nufi hanyar fita. Cikin sanyin murya yace.

"Bakomai kawai na tuna yanda Nana take nata ne bansan sanda ya bayyana ba"

Ga mamakin su duka biyun dariya safiyya tayi. A karo na farko tun rasuwar nana.

"Kasan akwai lokacin da ina fever. Naji nana shiru inata kira ashe tana kitchen.

Kasan me take?"

Da murmushi a fuskarshi ya girgiza mata kai. Dariya ta sake yi lokacin sun karasa bakin motar. Tsaye fu.ad yai yana kallonta yana son ta karasa bashi labari.

Cikin fuska take kallonshi.

"Kwai ta soyamun ta hado tea. She was 7 lokacin. Karka ga fuska ta sanda ta shigo dakin.

Ranar na fara jin tsoro a rayuwata. Ina tunanin data kone fa? Ko ta zubo ma kanta ruwan zafi.

Abinda tayi ya tabani sosai na kasa mata fada. Karka ga fuskata lokacin da nai tasting wainar kwan.

Goodness. It was awful"

Wanna karin fu.ad ne yai mamakin daga inda dariyarshi ta fito. Daga shi har ita dariya suke. Kamun wasu hawaye masu zafi su zubo ma safiyya.

"I miss her. Every second da bata nan ina jinshi a ko ina nawa wallahi"

Rikota yai jikinshi yana matse ta dam. Shi kanshi yanajin irin ciwon da take ji.

"Sofi kina da memories irin wannan ke. Banda su da yawa.

Dan Allah ki dinga sharing mun nima in samu? Zamu saba da kewarta a hankali. Komai zaiyi mana sauki"

Dagowa tai daga jikinshi tana goge fuskarta.

"Zan sharing maka duka. Duk wani babban abu da karami dazan iya tunawa"

Kai ya daga da murmushi a fuskarta. Itama kasa boye nata murmushin tayi. Tace mishi.

"As much as tunanin nana zai mana ciwo. Farin cikin dake tattare dashi mai girma ne"

"Ta tafi tabarmu da kewarta ne. Shisa zaiyi ciwo. Amman kuma tabar mana abubuwan farin ciki da yawa. Ina jina da sa.a sosai dana santa a rayuwata"

"Nima haka...... Muje gida dai"

Kai fu.ad ya daga yana sauke numfashi hadi da bude ma safiyya motar. Shiga tayi ya rufe sannan ya zagaya ya shiga shima.

*

Suna hanya sun kusa kai gida ma wayarshi ta hau ihu. Saida ya rage gudun da yake sannan ya lalubota daga aljihunshi.

Dubawa yai yaga lukman ne. Ya daga ya kara a kunnenshi. Kamun yace wani abu lukman yace.

"Fu.ad please ka gayama hajiya muna nan Aminu kano. Zainab ke labour.

Inata kiran wayarta baya zuwa"

Ware idanuwa fu.ad yayi.

"Wallahi nima na fito. Bara na kira momma sai taje su taho"

Kaman lukman zaiyi kuka yace.

"Please kai sauri. Ni kadaine a wajenta"

Katse wayar yayi. Fu.ad ya mikama safiyya wayar.

"Lukman ne. Kira momma kice su taho ita da hajiya. Zainab ke nakuda kuma ba kowa wajenta"

Da sauri safiyya ta lalubo number din momma. Allah ya taimaka ringing daya momma ga dauka. Fada mata tayi.

Sannan ta ce ma lukman.

"Da munje asibitin ma ai"

"Are you sure?"

Kai ta daga mishi tana masa kallon dake fassara tambayata ma kake. Lukman da zainab ake magana ba wasu ba.

*

Sun riga su momma zuwa asibitin. Lukman suka samu kallo daya zakai masa kasan yana cikin tashin hankali.

"Ya zainab din?"

Safiyya ta tambaya. Kai ya girgiza mata alamar bai sani ba. Kallon wajen fu.ad yake yana mamakin ganin lukman din ne kawai.

"Ina family dinta. Ka kira mamanta?"

Kallonshi lukman yayi. A sanyaye yace.

"Bata san babanta ba. Da cikinta ya rasu. Wajen haihuwarta mamanta ta rasu. Ita kadai ce wajensu"

Kai fu.ad ya girgiza. Yana jin wani abu daya tsaya mishi a wuya. Har safiyya kasa cewa komai sukai. Lukman ya yatsina fuska.

"Basu damu da ita ba. Lokacin da naje neman aurenta yi sukai kaman sun gaji da ita. Kaman daman jira suke su samu maraba da ita"

"Hmm duniya kenan. Rayuwar duka guda nawa ce"

Fu.ad ya fada yanajin wani tausayin zainab din ya cika zuciyarshi. Safiyya ta bude baki zatayi magana su momma suka karaso.

Kaman zuwansu wajen ya taho da sa.a. kamun ma suce wani abu. Nurse ta fito tana tambayar wanda suka kawo zainab.

Su dukansu suka nufe ta suna tambayar yaya. Murmushi tayi.

"Ta sauka lafiya. Ta samu baby girl. Suna cikin koshin lafiya. Zaku iya ganinta nan da mintina sha biyar in an shiga da ita dakin hutu"

Su duka hamdala suke. Cikin yanayin murnarsu fu.ad ya matsa ya kamo hannun safiyya ya rike. Dumtsewa nashi tayi tasan tambayarta yake ko she is okay.

Shisa ta amsa shi itama. Duk da halin rashi da take ciki bai hanata taya su zainab farin ciki ba. Haihuwa kyautar Allah.

Momma ta bude jaka ta zaro kudi taba nurse din hadi da yi mata godiya. Nan suka tsaya suna jira a fito da zainab din dan su shiga su ganta.

Aikam ana zuwa aka fada musu zasu iya shiga su ganta. Suka dunguma su dukansu. Tana kwance babyn na gefenta.

Momma ta fara daukar babyn ta mika ma lukman ya karba. Hamdala yai daya saukar da matarshi lafiya kamun ya kai kunnen babyn saitin bakinshi.

Kiran sallah yai mata cikin kunnen kamun da addu.o.i sannan ya matsa wajen fu.ad mika mishi ita yai.

"Kai mata huduba"

Ware idanuwanshi fu.ad yayi cike da alamar tambaya.

"Ko wanne suna yai maka"

Lukman ya fadi kasa kasa.

"Ya sunan maman zainab?"

Fu.ad ya fadi yana karbar yarinyar da yakejinta yar kararrama a hannunshi. Kallonta yake so cute. Yanajin wani abu a xuciyarshi daya kasa bama suna.

"Aisha"

Kai fu.ad ya daga ma lukman saboda bazai iya magana ba a yanayin da yakeji. Addu.o.i sosai yaima yarinyar ya mika ma lukman ita.

Yanajin yanda yai kewar dan nauyinta a hannunshi a iya mintinan datai wajen shi. Hajiya lukman ya mika ma yarinyar.

Ta karbeta itama tai mata addu.a sannan tabawa safiyya. Idanuwanta cike da tausayawa. Karbarta safiyya tayi ta kura mata idanuwa kamun tace.

"Zainab kamarku daya lukman ka bata mun daughter da guntun hanci"

Dariya sukayi. Suna jinjina ma karfin halin safiyya din. Da idanuwa lukman ya ke rokon hajiya da su dan bashi waje da zainab.

Tasan dalilin hakan ta dafa momma kamun ta mike. Ta fahimci so take subar dakin. Dan haka babu wani bata lokaci ita da momma suka fice.

Fitarsu ta fahimtar dasu safiyya. Ta mike hadi da bama zainab babyn.

"Allah ya raya ya sanya mata albarka"

Kasa dakai zainab tayi. Tana jin kunyar safiyya din. Dan murmushi tayi ta kalli fu.ad suka fice daga dakin suma.

Karasawa gefen gadon lukman yayi. A tsorace yake kallon zainab. Hannu yakai ya taba fuskarta.

"Sannu zee na. Allah ya miki albarka. Allah yasa kece matata har a aljanna"

Cike dajin dadin addu.arshi ta dafa hannunshi dake kan fuskarta

"Amin. Zan yi alfahari dee. Samun miji irinka sai an tona. Bazan taba manta karamcin da kaimun ba.

Kaime komai nawa kai....."

Saurin janye hannunshi yai daga fuskarta yana rufe mata baki.

"Shhhhh. Bana so. Banaso kina fadar haka. Abinda nai miki in kyauta ce kinbani linkinta da junior. Idan bashi ne kin ribamun riba mai girma.

Ina sonki zee. Zan fahimta in kin fasa niyyarmu. Wallahi bazan taba kallonki da abin ba.

Saboda cikin ba a jikina ya zauna wata tara ba. Bani nai miki naqudarshi ba.

Bana so kiyi abinda zakiyi nadamarshi dan farin cikina ba....."

Wannan karin ita ta rufe mishi baki.

"Ko da nake nakuda da niyyarmu daram a zuciyata dee"

Sauke numfashi yayi ya mike. Sumbatar ta yayi yana nuna mata godiyarshi. Yana daukar mata alkawarin kin manta wannan karamcin.

*

Leqo da kanshi yayi wajen dakin yace.

"Momma ku shigo. Fu.ad......"

Su momma wucewa sukayi. Ganin su fu.ad sun tsaya yasa shi fitowa daga dakin gabaki daya.

"Ku shigo mana"

"Zamu dawo lukman. Gida zamu tafi yanzun"

Girgiza kai yayi alamar bai yarda ba.

"Nidai ku shigo. Safiyya kema biyema fu.ad zakiyi ko?"

Kallon fu.ad safiyya tayi da idanuwa take rokonshi dasu koma din. Gani yake kaman ba zata iya handling emotions din ba shisa yake cewa su tafi gida.

Kai yadan daga mata. Ta saki hannunshi dake cikin nata. Suka shiga dakin a tare lukman na gabansu.

Tsaye sukai daga dan nesa su duka wannan karin sun rasa me ya kamata suyi.

Hada idanuwa safiyya tayi da zainab. Zainab din tai mata wani murmushi data kasa fahimtarshi. Kasa mayarwa tayi dan yanda take jinta.

Suna kallo lukman ya je wajen zainab tasa hannu ta miko mishi babyn. A hankali ya tako inda su fu.ad suke ya tsaya da babyn a hannunshi.

Juyawa yai ya kalli hajiya. Yaga alfaharin dake cike da idanuwanta. Farin cikin dake kan fuskarta dazai jima tunosu kawai na saukar mishi da nishadi.

Dan daga mishi kai tayi dake nuna me yake jira? Yayi kawai. Juyawa yayi ya sauke idanuwanshi cikin na fu.ad.

Fuskarshi dauke da wani yanayi yace.

"Lukman ni me zan da yara? Idan ina bukatarsu ga naka nan zaka haifa. Ga  haneef ga su pha.iza zan gansu"

Sosai yake kallon idanuwan fu.ad din saida yaga alamar ya tuna exact maganganunshi shekarun da suka wuce. Yaga dana sani da nadama dake cikin idanuwanshi.

Sannan yace.

"Yes rabin maganarka babu karya a ciki fu.ad. kana da mu. Kuma yanzun kana bukatar ya'ya. Saidai daya kawai zamu iya haifa maka......"

Lukman ya karasa maganar yana mika mishi babyn. Kallon safiyya fu.ad yayi sannan ya kalli lukman ya kalli babyn.

Muryarshi na rawa yace.

"Me kake nufi?"

Dan ya kasa fahimta. Duk da kunnuwanshi sunji maganganun lukman. Zuciyarshi taki yarda ta karbe su.

"Kaji ni ai. Baby muka haifo maka ni da zainab...."

Hannu fu.ad yakai kan kirjinshi yana dafe inda zuciyarshi ke wani irin tsalle kamar zata fado.

Momma ya kalla ita kanta mamaki ne karara a fuskarta. Ta kalli hajia idanuwanta cike da tambaya da hawaye.

Tana so taji ko da saninta lukman zaiyi wannan abin. Kai hajiya ta daga mata hadi da fadin.

"Wacece ni in shiga tsakanin yan uwa?"

Hawayen da suka zubo ma momma ta goge tana fadin.

"Na rasa abinda zan fada"

"Ki sanya musu albarka"

Kai momma ta daga ma hajiya tana kallon su fu.ad wanda dakyar ya iya cewa.

"Lukman please. Ka daina mun irin wasan nan"

Kallon baka da hankali ko? Lukman yai mishi kamun ya sake mika mishi babyn.

"Ka karbeta fu.ad....."

Jikinshi ko ina bari yake. Idanuwanshi cike taf da hawaye ya mika hannu ya karbi babyn.

Safiyya ya kalla. Ta matso kusa dashi tana sa hannuwanta jikin nashi suna rike babyn tare. Ta kasa tsaida hawayenta.

Sun kuma kasa daina kallon babyn. Dakyar fu.ad ya dago da kanshi yace ma lukman.

"Wallahi zamu riketa da kyau. Zamu kula muku da ita"

Zainab data dafa gadon ta mike zaune tace.

"Mu asuwa? Zaku kula da yar'ku dai."

Kallon ta sukayi sannan suka kalli lukman. Suna son jin ko gaskiya ne abinda ta fada.

Daga mishi kai lukman yayi.

"Ba riko muka baku ba fu.ad. Aisha fu.ad Arabi. Mu muka haifeta. Amman yar'ka ce fu.ad.

Allah ne shaidarmu akan wannan. Zamu amsa sunan masu haihuwarta ne kawai."

Hawayen da suke idanuwan fu.ad suka zubo. Bai kokarin gogesu ba saboda yanajin yanda wasu ke sake fitowa.

Kuka suke sosai shida safiyya suna rike da yarinyar har lokacin. Shi kanshi lukman kukan su yasa hawayen zubo mishi.

Harsu hajiya ma da zainab din. Hannu lukman yasa ya goge fuskarshi.

"Enough please."

Girgiza kai fu.ad yake. Saboda ya kasa tsaida su. Bai taba tunanin wannan karamcin daga wajen lukman ba.

Bai taba tunaninshi daga wajen haneef bama balle lukman. Allah kenan. Ya karbi nana cikin Hikimar shi kuma ya basu wata kyautar.

Kyautar dako a mafarki basu taba zaton ta ba. Mikama safiyya babyn fu.ad yai duka yasa hannu yana goge hawayen dake bin fuskarshi.

"Lukman........"

"Shhhh inhar zumuncin mu yakai inda na dauke shi zakai shiru ba zaka ce komai ba"

Shiru fu.ad yai yana runtse idanuwanshi. Takawa yai ya karasa wajen zainab. Tsugunnawa tai kan gwiwoyinshi.

Hannuwanshi na rike da gefen gadon. Kasa ce mata komai yayi. Ya kife kanshi jikin gadon kawai hawaye na ci gaba da zubi mishi.

Me zaka ce ma wanda ya dauki farin ciki ya baka? Babu wasu kalamai.

Muryar zainab na rawa tace.

"Nagode da karamcin dakaimun. Nagode daka sakama yarka sunan mahaifiyata.

Allah ya raya muku ita"

Dago kai yayi ya kalli momma yace.

"Momma kinji itace takemun godiya wai. Really? Wai nine nai mata karamci.

Momma da wanne baki zan musu godiya? Wallahi ban cancanci wannan karamcin daga wajensu ba sam"

Hajiya ce tai mishi dakuwa.

"Gidanku fu.ad da irin maganganun nan. Kar in sake ji. Ka tashi ku wuce gida ma.

Mu ma da zainab ta warware gidan zamu tafi"

Mikewa fu.ad yayi. Ya karasa inda lukman yake tsaye. Hugging dinshi yai. Lukman ya ture shi yana dan tari.

"Maza ragargazamun kashi kar inci naman suna da kyau"

Dariya fu.ad yayi yana girgiza kai. Safiyya ya kalla datake takowa ta karaso wajensu.

Lukman ta kalla.

"Allah ya karramaka linkin yanda kai mana. Allah ya baka aljanna"

"Amin safiyya. Allah ya jikan Nana"

Kai ta daga mishi hawaye na zubo mata. Karasawa tayi ta zauna gefen zainab.

Hannunta daya rike da babyn dayan kuma ta saka shi cikin na zainab.

"Mahaifiya tace kadai zatai mun irin abinda kikaimun.

Allah yabarki da mijinki yasa zamanku har a aljanna. Zamu kula da ita na miki alkawari"

Murmushi zainab tai mata.

"Kome zaisa lukman farin ciki. Amin Allah ya jikan Nana ya raya muku baby"

Kai safiyya ta daga tana jin hawayen na sake zubo mata kamun tace

"Ki shayar da ita. Kar a dauki alhakinta. In yaso sai mu karba in....."

Katse ta zainab tayi.

"Banda enough milk. Ko junior madara yasha. Karki damu"

Lumshe idanuwa safiyya tayi tana sauke ajiyar zuciya. Kai kawai ta daga ma zainab ta mike. Fu.ad ta kalla.

Basu da sauran abinda zasu fada. Wannan karin sun manta da su momma dake wajen. Hannunta safiyya tasa cikin nashi suka juya suka fice.

Zainab ta kalle su tana sauke numfashi. Tana jin kewar yarta har ranta. Sai dai tana da yaqinin zasu kula da ita fiye da su ma kila.

Kallon lukman tayi. Kalar yanda ya kalleta ya wanke mata duk wani shakku daga zuciya.

*

Basu bar asibitin ba saida suka nemo  doc din yara ya basu shawarwarin dazai basu tukunna.

Suna mota safiyya rungume da babyn. Lokaci lokaci fu.ad na juyowa ya kalle su. Sun kasa cewa komai har yanzun.

Kamun fu.ad ya kori shirun da fadin.

"Muje mu siya ma Mimi kaya tukunna"

Kallonshi safiyya tayi.

"Mimi?"

Kai ya daga mata hadi da fadin.

"Sunan maman zainab ne. So zamu boye ko daman.

Kuma nana tace inda tana da kanwa zata dinga kiranta mimi"

Murmushi safiyya tayi.

"Nana ga kanwa kin samu. Saidai Allah baiyi zaki ganta ba"

Jin rawar da muryar safiyya take yasa fu.ad fadin.

"Mimi kinji mumynki ko? Big sis dinki ba zata taba ganinki ba. Amman ke zaki ganta. Ina da pictures da labarai da yawa"

Murmushi safiyya ta sake yi. Tana jin su inna kawai take son tai magana dasu ta fada musu sauyin daya shigo rayuwarta.

Ta nuna musu kyautar Allah yawane da ita. Inya jarabceka badan ya manta dakai bane. Saidan Yafi kowa sonka ne.

*

Aikam biyawa sukayi. Siyayya kawai fu.ad yake kaman baisan wahalar neman kudi ba.

"Ya isa haka"

Cewar safiyya. Girgiza mata kai yayi yana dakuna fuska.

"Bafa a baby zata zauna ba. Inta kara girma zamu dawo. Kaga wanna zasu zama waste. Abarsu haka"

Jim yadanyi kamun ya jinjina mata kai cikin yarda da abinda tace din. Zuwa sukayi suka biya kudin kayan aka diba aka zuba musu.

Boot ya cika dam. Kaya har bayan motar. Suka shiga sannan safiyya tace.

"Mimi akwai hakuri. Har yanzun batai kuka ba. Bacci take tayi ma. Da naso muje gidansu inna mu nuna musu ita.

Mu dai je gida in hada mata madara tukunna.

Inmun huta sai muje ko"

Kai ya daga yace mata.

"Ke kika riketa dazun. Yanzun ni zan riketa kiyi driving"

Kafada ta makale alamar bata yarda ba.

"Inji waye? Kai zakai driving"

Shagwabe fuska fu.ad yayi.

"Please......"

Bude motar tayi ta fita tana zagayawa ta bude shi. Fitowa yayi ta bashi Mimi sannan ta shiga wajen daya fito shikuma ya zagaya.

A hankali ya shiga yana rufe kofar hadi da kallon mimi da take ta baccinta kamun safiyya ta tayar da motar su tafi.

*

Fitowa tai da madara a hannunta ta samu fu.ad a tsaye inda tabarshi tun shigowarsu.

Hankalinshi kwance yake zuba ma mimi labari. Dan murmushi tayi. Yanayin da take ji bazai barta ta fada mishi mimi bata jin me yake fada ba.

Karbarta tayi ya shiga bedroom din yayo alwalar sallar la.asar ya fito ya wuce masallaci. Jin gidan take yi shiru.

Tasan da gaske Nana ta rasu. Tai accepting hakan. Amman wani bangare na zuciyarta gani yake kaman Nana zata fito daga dakine tana tambayarta inda ta samo baby.

Lumshe idanuwanta tayi tana maida hawayen da take ji.  Addu.a sosai taima Nana. Mimi nagama shan madarar ta sake komawa bacci.

Taso ta sake mata wankane. Saita hakura tabarta ta huta. Dan gadonta da suka siyo ta dauka  sannan ta wuce bedroom din.

Saida ta saka ta a ciki ta lillibeta sannan ta shiga bandaki ta dauro alwala ta fito tai sallar la.asar.

*

Tana kwance kan gadon abinta hannunta daya kan gadon mimi ta dora shi. Sosai tunanin rayuwa take da abinda ke cikinta.

Taji an hawo gadon an riketa ta baya. Sauke numfashi tayi.

"Banji shigowarka ba"

Sumbatar ta yai a kai ta baya sannan ya amsa da.

"Bana son tunanin nan please"

Shiru tayi. Tunani kam dole ne sai a hankali tukunna. Jin yanda ya riketa yasa ta dora hannunta kan nashi tana shirin zame jikinta.

"Sofi. I miss us. Please....."

Shirun da tayi ya bashi amsar da yake bukata. Cikin mintina ya fara nuna mata kalar kewarta da yayi shekarun nan.

Yake nuna mata yanda soyayyarta take tare dashi duk nisan da sukayi.....!

**

Bai iya fita magrib masallaci ba. A gida yaja musu shida safiyya da wata kalar kaunarta ke masa yawo.  Ga wata nutsuwa.

Tare suka shiga toilet din da abin wankan da suka siyoma mimi. Safiyya tai mamakin ko uhm mimi batayi ba. Tace ma fu.ad

"Kasan Nana kukan wanka take?"

Ware idanuwa yayi sannan ya kwace da dariya.

"Nana da kukan wankan. Baki fadamun ba ai dana tsokane ta"

Murmushi safiyya tayi. Jin yai shiru yasa ta dagowa ta kalle shi. Ruwan tadan diba ta watsa mishi a fuska. Da sauri ya kawo hannunshi ya kare yana fadin.

"Sofi mana....."

Ware mishi idanuwa tadanyi kamun ta maida hankalinta kan mimi da take sakawa a towel.

"Kai kace banda yawan tunanin"

Kallonta yai yace.

"Ina jin kewarta sosai...."

"Nasani nima haka. Allah ya bamu mimi. Duk da samunta bazai hana mana kewar nana ba.

Zai bamu sabon farin ciki."

Kai ya jinjina mata.

"Me zamu ci? Wani abu simple dai"

I
ta batama jin cin komai saidai tasan in taki shima haka zai kwana tun breakfast din da momma ta takura su suka ci da safe.

"Ka zauna da mimi karmu barta ita kadai. Sai in dafa mana indomie"

Karbar mimi din yayi yana kallon yanda tayi kyau cikin fararen kayan sanyin da aka saka mata. Wani irin kaunarta ke shigarshi a hankali.

"Mi daughter"

Ya fadi a hankali kaman yana son sake tabbatarwa tashi din ce. Babu mai kwace mishi wannan kyautar.

*

Indomie din sukaci. Sukai sallar isha.i. Ya zauna da mimi safiyya ta watsa ruwa sannan ta fito shima ya shiga.

Tana kwance kan gadon ya hau ya kwanta gefenta yana nazarin fuskarta.

"Gadon inajin shi very empty babu Nana."

Baice komai ba ya sauka daga kan gadon. Mimi ya dauko daga nata gadon a hankali. Har mamakin ina ya iya daukar jariri yake.

Towel dinta ya mika ma safiyya yana nuna mata ta shimfida. Batai musu ba ta shimfida. Ya kwantar da mimi tsakiyarsu sannan ya kwanta.

Murmushi yadan mata.

"Better?"

Kallon mimi tayi ta lumshe idanuwa tana ma Allah godiya kamun ta bude su kan fu.ad.

"Much better"

Sake gyara kwanciya yayi yana kallon fuskarta yace.

"Ya kikayi all the years da bana nan?"

Girgiza mishi kai tayi.

"Bana son tuna baya. Ina son kallon gaba ne kawai"

Shagwabe fuska yayi.

"Ina son ji ne"

Kai ta daga a hankali ta fara mishi bayani da fadin.

"Ba wani abu much fa. Sati biyu bayan nagama kukan nagama zuba idanuwa baka dawo ba.

Nakoma school. Ina amfani da kudin dake cikin gidan inayin komai da nake bukata kamun su kare.

Cikin Nana bamai wahala bane. Dan bana wani amai ko wani abu. Ina cin abinci sosai sosai dai. Anty Laurat ta fara cemun ina da ciki.

Kamun in noticing Changes din da kaina. Saina fara dibar kudin dake bank. Muna zuwa da ita mu dauko.

Tun ina mamakin yanda suka ki karewa har nazo nasan kaine kake turowa. Really bana son tuna duk wannan.

Kawai i was so happy bayan haihuwar Nana and sad da baka nan. Sad da bansan ko inkana nan zaka so ta ba.

So koma yanai rayuwa ba abin dubawa bace a yanzun. Kasan abu daya koda kai nisa. Ko yanda bana son in fada.

Da kulawarka na rayu. Da kulawarka muka rayu duk shekarun nan ni da Nana. If bakai tunanin turo mun kudade ba........"

Sauke numfashi tayi tana kasa karasawa. Muryarta a sarke tace.

"Please mubar maganar nan. Baya ta zauna a baya. Mu duba gaba kawai"

Hannunta ya kamo ya dumtse yanajin wani abu ya tsaya mishi a wuyanshi.

"Kisani wallahi dazan iya. Da inada iko dana koma baya na canza komai"

Dan murmushi tayi.

"I know. I.... I love you"

Ta fadi. Ware idanuwanshi yai da hakan yai mata yanayi da nana sosai.

"Thank you."

Ta daga mishi kai hadi da hamma. Dariya yai. Itama haka kamun suyi addu.a su kwanta. A karo na farko tun rasuwar nana da suka samu bacci.........!

****

"Ina zamuje baka fadamun ba har yanzun yaya farhan"

Kallonta yadanyi sannan ya maida hankalinshi kan tuqin da yake da murmushi a fuskarshi.

"Home. Your home"

Da rashin fahimta tace.

"Bangane ba"

"Zaki gane nuriyya....."

Girgiza kai kawai tayi ta gyara kwanciya cikin kujerar. Ga mamakinta corner suka shiga.

Bata sake mamaki ba saida taga sun nufi wani katon gida an bude musu. Kallon farhan take har yai parking. Sannan ya juyo ya kalleta.

Fuskarshi da wani farin ciki yace mata.

"Kin shirya ganin family dinki"

Hannu takai tana rufe bakinta cike da mamaki. Idanuwanta na kawo hawaye.

"Da gaske yaya farhan"

Ya daga mata kai.

"Da gaske nuriyya. Family dinki na jiranki"

Ko ina jikinta rawa yake. Ta kasa cewa komai saboda gani take data sake bude baki zuciyarta fitowa zatao saboda dokawar da take.

Tana kallo har farhan ya fita ya zagayo ya bude mata. Hannunta ya kamo ya fito da ita. Dakyar kafafuwanta ke daukarta.

Dam ta rike hannun farhan dake cikin nata. Ta kasa yarda. Gani take da tai wani wrong motsi wannan mafarkin bacewa zaiyi.

Kamata yai suka hau steps ukku dazai kaika kofar gidan sannan suka tura kofar. Farhan ya shiga da sallama.

Muryoyi taji fiye da biyu sun amsa farhan. Idanuwanta cike suke taf da hawaye ba sosai take ganinsu ba. Blinking tayi tana fito da hawayen da suka tarar mata.

Sannan ta ware idanuwanta tsakiyar falon. Kan wata mata idanuwanta suka fara sauka. Ta kuma kasa janye su saboda yanda take jin zuciyarta na wani irin abu.

Wata irin kaunar matar na shigarta data kasa fahimta. Kaman daman can an halicci zuciyarta ne kawai dan ta kaunace ta.

A hankali take takawa zuwa inda matar take tsaye idanuwanta itama kafe kan nuriyya da batasan tana karasawa ba.

Tsakiyar falon suka hade da matar. Hannunta takai da yake rawa tana taba fuskar nuriyya.

"Nuriyya....."

Ta fadi. Hannunta dake fuskarta nuriyya ta kama ta dumtse tana jin wani yanayi da bata tabajin shi ba a rayuwarta.

Batasan lokacin data rungume matar ba. Kuka suke a tare. Ko ba a fada mata ba zuciyarta tasan wannan mahaifiyarta ce. Sosai suke kuka kamun wani babban mutum dake tsaye yace.

"Hajiya aikin saketa muma muganta ko"

Sakinta hajiya karima tayi. Tana goge fuska kawai bata taba sa ran zata sake ganin yartata ba. Duk da kullum da tunanin halin da take ciki take kwana take wuni.

Takowa yai. Hannuwanshi yasa ya tallabi fuskar nuriyya. Yana kallon yar tashi da suka cire rai da sake ganinta sai yau da farhan ya same shi yake mishi tambayoyi.

Hawaye yaji sun zubo mishi kamun yai hugging nurriya suna ma Allah godiya. Sun dauki mintina a hakan kamun ya dago nuriyya yana goge mata fuska.

Hannunta ya kama ya shiga janta wajen yayyanta maza har biyar. Sai kannenta su biyu maza. Ita kadaice ya mace da Allah ya basu.

Yinin ranar cikin yan uwanta tayi shi. Dan farhan tafiyarshi yayi. Saidai bata yarda ta kwana ba. Duk yanda take so da yanda yan uwanta suka so.

Ba zata iya barin farhan shi kadai ba bayan wannan halaccin dayai mata. Tai alkawarin shima saita sa ya nemi nashi yan uwan dan yaji abinda take ji itama.

Wannan farin cikin wajen shi da ban ne. Girman kaunar yan uwantaka bata taba haduwa da wata. Allah ne ya hada jini daya waje guda.

Shi kadai Yasan hikimar haka. Zumunci abune mai girman gaske.......!

*#TeamAS*

No comments:

Post a Comment