Thursday 4 May 2017

AKAN SO 28

*💘💖AKAN SO💖💘*

~Written by~ :Luβπα Sufyαπ
 

            28

*Thank you for all your support and comments. Daga yanzun akan kowacce chapter zan saka sakkoni ukku da sunayen wanda suka turo mun su. Meye naku ra.ayin AKAN SO?*

Tana yin sallar la.asar ta koma falo ta zauna tana kallo. Tun da suka ci abinci fu.ad ya sake fita.

Anan ya sameta da ledoji a hannu da safiyya tasan kayan ciye ciye ne a ciki. Tun tana mamakin kalar cin abincin fu.ad harta daina.

Kasa ya zauna yana ajiye komai. Robobin ice cream ya fiddo guda hudu ya ajiye. Ya kalli safiyya da idanuwanta ke kanshi.

"Sakko mu sha"

Batai mishi musu ba ta sakko. Ta dauko roba daya ta bude. Harya soma koya mata yan ciye ciyen nan.
Bata ko shanye rabi ba ta ajiye.

Dan yanzun tana iya fara tari. Sam basa shiri da sanyi.

"Kinyi me kenan?"

Fu.ad ya bukata yana ajiye robar daya shanye ya dauki wata ya bude.

"Na koshi. Saika yi mura ko?"

Ware idanuwanshi yai akanta. Yana ci gaba da shan ice cream dinshi. Hankalinshi ya maida kan film din da take kallo na hausa zuri.a.

"Wai duk yaran ta ne wannan ukkun?"

Ya tambayi safiyya ta amsa shi da.

"Eh mana. Abin sha.awa ko"

Yamutsa fuska yai hadi da fadin.

"OH-OH ..."

Da mamaki take kallonshi.

"Basu burgeka ba kenan"

Girgiza mata kai yayi.

"Ko kadan...."

Dariya ya bata.

"Inka haifi naka zasu burgeka"

Ware idanuwanshi yai akanta yana fadin.

"Wa?  A duniyarmu babu yara sofi. Daga ni sai ke"

Dariya ya bata. Fu.ad akwai zolaya ta fadi a ranta bata ce mishi komai ba har akai magrib. Sannan ya fice masallaci.

Kwashe robobin ice cream din daya shanye guda uku tayi. Sauran nata kuma ta bude fridge ta saka in mama indo ta shigo ta bata.

Kamun ta wuce dakinta.

*

A kwance ta fito daga wanka ta same shi kan gadon yana danne danne da wayarta.

Zama tayi gefenshi. Ya dago ya kalle ta. Sosai yakai kanshi jikinta yana shakar kamshinta.

"Wanne irin turaruka ne wannan?"

Dariya tadanyi.

"Bansan sunan su ba. Anty fatima ta hadomun randa mukaje gidan tan nan"

Sake shaka yai yana wani sauke numfashi. Sun mishi dadi sosai.

"Nima a shafamun"

Hannunta ta goga a fuskarshi.

"Gashi nan"

Rike hannun yai.

"Wayau ko sofi?"

Boye kanta tai a jikinshi. Sumbatarta yai sannan ya jata sosai suka koma tsakiyar gadon.

Wata irin soyayyarshi yake nuna mata mai tsayawa a zuciya. Dakyar yakai hannu jikin switch din ya kashe musu kwan..........."

*

"I love you so so much sofi. Nagode...."

Yake fadi yana sumbatar kanta. Ya wani riketa kamar za.a kwace mishi ita.

Tun dazun ya fadi mata i love you din nan yafi a kirga. Ta kasa cewa komai saboda sanshi da kunyarshi da suka hadar mata.

"Tashi muyi wanka sofi"

Wani makalewa tai a jikinshi. Ko ina ciwo yake mata. Kai ta girgiza mishi. Yar dariya yayi ya mike daga kan gadon.

Wanka ya shiga yayi. Yana fitowa ya goge jikinshi ya hau kan gadon. Dago ta yayi.

Sam taki hada idanuwa dashi. Cik ya dauketa yana nufar toilet da ita.

"Zan iya zuwa da kaina........"

Cikin fuska ya kalleta.

"Kin tabbata?"

Kai ta daga mishi. Bai sauketa ba sai daya kaita cikin bandakin sannan ya janyo mata kofar a hankaki.

Wardrobe ya bude ya dauko mata wata rigar baccin. A hankali ya tura bandakin ya mika mata.

Sanda ta fito bakin kofar bandakin ta same shi a tsaye. Hannunta ya kama suka hau gadon tare.

Riketa yai jikinshi. Wata sumba mai taushi ya manna mata. Hannu tasa tana ture shi.

"Yi hakuri....."

Ya fadi yana sauke numfashi.
"Bacci nake ji......"

Ta karasa muryarta can kasa. Gyara musu blanket yai yai musu addu.a. Cikin sanyin murya yaji ta sake rike shi tace.

"Tun daga ranar daka shigo rayuwata komai ya dai daita..."

Da murmushi a fuskarshi ya ce.

"Bansan akwai abinda na rasa ba a tawa rayuwar saida na mallake ki..."

Sumbatarta yai a goshi yana jin numfashinta ya canza alamar bacci ya dauketa kamun shima wani ni.imtaccen bacci yai gaba da shi.

*

Sama sama yake jin kiran asuba. Dakyar ya iya tashi ya shiga bandaki yai alwala. Bai tashi sofi ba dan yasan shiya hana mata baccin kirki jiya.

Ya fita masallaci. Yai mamaki daya dawo ya sameta zaune kan kafet. Karasawa yai ya zauna gefe.

A kunyace tace mishi.

"Ina kwana...."

Dan rankwafa kanshi yai yana kallon fuskarta da taki dagowa.

"Sofi ki kalle ni mana"

Hannu ma tasa ta rufe fuskarta tana dariya. Janta yai jikinshi.

"Nagaji da kunyar nan fa. Taso kiga in kara rage ta......."

Ture shi tai tana dariya.

"Kin tashi lafiya? Ba inda ke miki ciwo ko?"

Kai ta daga mishi alamar babu. Tana mikewa.

"Ina zaki?"

"Zan shiga kitchen in hada maka abinda zaka karya kamun ka tafi"

Riko mata hannu yayi.

"Sai sha goma zan fita. Barshi sofi mudan kwanta. Anjima in na shirya zan siyo mana wani abu"

Hamma tayi kamun tace.

"Allah ya kaimu"

Kallonta yake sosai. Yana sake gode ma Allah daya bashi ita.

"Bacci ko?"

Ya bukata. Daga mishi kai tayi alamar eh. Mikewa yai ya kama hijab dinta ya cire ya ajiye gefe daya yana fadin.

"Kuma hakuri zaimun saboda na fishi bukatarki"

Murmushi tayi tana sadda kanta kasa. Hannunshi ya dora saman kafadunta yana mata wani irin kallo.

"Say mi' name sofi. Ina son ji akan lips dinki"

Murmushin dai ta sake yi. Hade space din dake tsakaninsu yayi. Cikin kunne yake gaya mata kalaman da sirri ne tsakaninsu.

Kanta ta boye cikin kirjinshi tana dariya kamun ya soma aika mata sakon da yasa daga shi har ita tsayuwar ta gagare su. Dan haka ya jata kan gadon.....!

*

Takalminshi yake daurawa sofi da comb dinshi a hannu yanajin yanda take yamutsa mishi sumar kanshi da comb din.

A dole taje mishi take tana kokarin kwantar da ita baya. Karasa daura takalmin yai ya riko hannayenta duk yana sauke idanuwanshi cikin nata.

"Kwana biyu sun mun kadan....."

Ta fadi can kasan makoshi. Ya lumshe idanuwa. Tun kamun su hada gado ma kewarta na azabtar dashi ballantana yanzun.

Yasan sai ya fita shiga damuwa. Mikewa yai ya zaro wayarshi daga aljihu.

Kumatunshi ya hada da nata ya daga camera din yana daukarsu hoto. Wani kuma ya rungumota ta baya.

Sannan ya mayar da ita aljihu. Yai cupping fuskarta.

"Tafiyar lokaci ne kawai abinda ke rike ni inhar nabar nan. Saboda nasan da duk mintin dazai wuce da kusantar kwanakin da suka ragemun in sake ganinki"

Hannunta ta dora kan nashi tana kokarin tarbe hawayen fuskarta.

"Banda kallon turawa wanda suka fini kyau....."

Dariya ta bashi ba kadan ba. Yana dariya yace.

"Sofi idanuwana kadai zasu kalle su. Na miki alkawari zuciyata na tare dake komin nisa"

Har ranta ta yarda da maganarshi. Tanajin tsakanin jiya da dare da yau da safe soyayyar daya nuna mata babu shakku a cikinta.

Hannunta ya kama ya dora kan kirjinshi dai dai inda zuciyarshi take.

"Karfin  dokawarta zamanki ne a ciki"

Batasan lokacin data cire hannunta ba ta sumbaci inda yabari. Cikin idanuwa ta kalle shi.

"Ina sonka. Ina sonka sosai"

Hugging dinta yai yana jin wani irin emotion da baisan ta yanda zai fara fassara shi ba.

Kofa ta raka shi.

"Allah ya tsaremun kai a duk inda kake. Allah ya bada sa.a ya dawomun dakai lafiya......"

Ta karasa maganar muryarta na rawa. Girgiza mata kai yake. Baya son hawayen dayake gani cikin idanuwanta.

Sumbatarta ya sake yi sosai yana kokarin shanye duk wata damuwa da take ciki.

"Sai munyi waya"

Kai ta daga mishi tana kallo harya fice yai wajen mota inda driver ke jiranshi.

Ajiyar zuciya ta sauke tasa hannu ta goge hawayen da suka zubo mata. Sannan ta koma cikin daki ta kwanta.

Kiran fu.ad kawai ta tsaya jira su sake yin sallama kamun wani bacci mai nauyi ya dauke ta cike da mafarkin fu.ad.

****

In tai duba yanda kwanaki suke wucewa suna zama satika. Yanda satika ke wucewa zuwa watanni abin har mamaki yake bata.

Wai yanzun har sunyi watanni bakwai suna cikin na takwas da fu.ad.

Kusancin su na bata mamaki sosai. Dan ji take yi kamar sunyi shekaru ne ba watanni ba. Banda kewar su inna da take manne zuciyarta tana tunasar da ita abinda suka rasa na cikar farin cikinsu.

Zata iya rantsewa babu matar data kaita sa.ar miji. Danma lokaci na musu kadan. Duk da hakan baya hana fu.ad nuna mata doyayarshi.

A watannin nan duk bayan sati takwas yake zuwa yai kwana biyu. A dawowarshi ta biyune ya bude mata account.

Da kanshi suka je ya koya mata yanda zata cire kudi ta ATM wanda bai mata wuya ba saboda ci gaba sosai data samu a bangaren karatu.

Su khadija ke bata shawarar ta tafi account class dan abu biyu zaka dauka daman a aji hudu.

Safiyya art ne da account nata combination din kuma sunga tafi gane calculations.

**

Wannan dawowar ya karanci akwai damuwa tattare da safiyya. Kyaleta yai saida ya nutsu ya huta sannan.

A hankali yace mata.

"Sofi meke damunki?"

Kallonshi tayi a sanyaye ta girgiza kai alamar babu komai.

Tashi yai daga kujerar da yake a koma ya tsugunna gabanta ya kalle ta sosai.

"Wa kike dashi dazai ji damuwarki fiye dani?"

Wasu hawaye masu dumi suka zubo mata. Ware idanuwa fu.ad yai.

"Subahanallah sofi dan Allah menene?  Ko na miki wani abu ne?"

Kai ta girgiza mishi alamar a.a. ya koma gefenta ya zauna ya riko hannunta.

"To menene?"

Kallonshi tai wasu hawayen na sake zubo mata.

"Ina kewar su inna sosai. Kuma kwana biyun nan ina yawan mafarkinsu.

Kawai ina son sanin halin da suke ciki ne......"

Ta karasa tana kwantar da kanta a jikinshi. Kamata yai yana jin wani iri a zuciyarshi. Kamata yai ya mikar da ita tsaye.

"Muje ki shirya mu tafi"

Da sauri tace

"Ina?....."

Ba wani alamar razana yace

"Wajen su inna. Abinda ya kamata inyi ne tuntuni. Rashin son ganinki cikin damuwa ya hana"

A tsorace take girgiza mishi kai. Riketa yai a jikinshi. Kuka take tana tuno yanda su inna suka koreta.

"Sofi please. Bana son kukan nan ko kadan. In bamuje ba ba zaki daina ba"

Kankame shi tai tana girgiza kai.

"Tsoro nake ji"

Kissing dinta yai a goshi yana kamata zuwa bedroom.

"Ina tare dake. Ni da ke zamu iya yin komai a tare. Zamuje in su inna sun karbemu fine. In basu karbemu ba zamu dawo.

Zamu sake komawa wani lokaci. Zamuyi ta komawa har sai sun karbe mu"

Da maganar shi ta samu dan kwarin gwiwa ta shiga bandaki ta wanke fuskarta. Ta fito ta dauki mayafinta tasa takalmi suka fita.

*

Wani irin dokawa zuciyarta take saboda tsoron da take ji. Tun fu.ad na kokarin janta da hira harya hakura.

Sai dai lokaci lokaci zai kai hannu yadan taba nata yana son nuna mata yana tare da ita a duk abinda zai faru.

Zuciyarta ci gaba tai da dokawa fiye dana da ganin anyo kwanar layinsu. Komai take ji yana kwance mata.

Harya karasa kofar gidansu yai parking. A tsorace ta kalle shi idanuwanta cike da hawaye. Hannu yakai ya rike nata. Cikin sanyin murya yace.

"Be strong sofi. In shaa Allah komai zai zo da sauki"

Hawayen da suka zubo mata ta goge. Tana kallo ya fita daga motar ya rufo. Zagayowa yayi ya bude mata.

Ganin taki fitowa ne yasa ya kamo hannunta ya fito da ita. Gabanta faduwa take. Ji take kaman ta ruga ta koma mota.

Idan su inna suka sake korarta fa? Suka sake mata abinda yafi na farko. Wani bangare na zuciyarta kuma yake fada mata bakomai ai. Ko dai sun sake korarta tagansu.

Taga suna nan lafiya. Hankalinta saiya dan kwanta. Tare suka taka har kofar gidansu. Kafafuwanta sun mata wani irin nauyi.

Bude baki safiyya tai zatai masa magana dai dai fitowar wata yarinya daga gidan da zata kai shekaru sha biyar.

Da mamaki safiyya ke kallonta dan zata rantse bata taba ganinta ba kaman yanda ita ma take kallon safiyyar.

Wani miyau ta hadiye sannan tace ma yarinyar.

"Sannunki...."

Ta amsa da.

"Ina wuni"

A tsorace safiyya ta kali fu.ad sannan ta maida dubanta zuwa ga yarinyar.

"Su inna suna ciki?"

Da mamaki yarinyar tace.

"Innarmu kike nufi?"

Safiyya ta girgiza mata kai.

"Aa masu gidan"

Cikin rashin fahimta yarinyar tace

"Mune masu gidan ai"

Da sauri safiyya ta tureta ta shige cikin gidan bata damu da yanda fu.ad ke kwala mata kira ba.

Wata mata ta samu tana jan ruwa. A tsorace ta saki gugar ya koma ciki ganin safiyya babu ko sallama.

"Ina inna?"

Ta tambaya tana karema gidan kallo. Cike da tsoro matar tace.

"Wacece ke? Daga ina haka babu ko sallama wacce innar?"

Girgiza kai safiyya take. Zuciyarta na barazanar barin kirjinta. Kallon matar tayi idanuwanta cike da hawaye tace.

"Dan Allah masu gidan nake nema"

Sai lokacin matar ta gane inda ta dosa.

"Allah sarki. Mu muka siyi gida. Watansu biyu kenan da tashi"

Wani abu safiyya ke ji yana mata yawo cikin kunnuwa. Da gudu ta fito ta samu fu.ad dayake kai kawo a kofar gidan.

Da sauri ya kamata ganin tana shirin shidewa. Fuskarta yake dan bubbugawa.

"Sofi menene?"

Dakyar numfashinta na wani sama sama tace.

"Sun tashi. Basa gidan...... Wallahi basa nan"

Ware idanuwa fu.ad yai. Kamun yadan saita kanshi sanin tana bukatar shi.

"Aa sofi. Ki kwantar da hankalinki. Babu inda suka je. Ki jirani anan bari in tambayo mutanen can"

Kai kawai ta daga mishi tana kallonshi ya tsallaka inda majalissar take.

Yana magana dasu. Wani irin dokawa zuciyarta takeyi. Yana tahowa ta kasa jira ya karaso ta taka suka hade.

Fuskarshi kawai ta kalla zarginta ya tabbata. Tsuggunewa tai a wajen tana sakin wani irin kuka.

Rikota yai dakyar. Ya jata ya bude motar ya rufe saboda mutane sun soma kallonsu sannan ya zagaya ya shiga shima.

Saida ya ja motar suka fita daga unguwar gabaki daya suka hau titi tukunna yai parking ya nutsa hankalinshi kan safiyya dake zaune ta hade jiki tana wani irin kuka.

Dafe kai yayi. Tuqa motar yai saboda yamma ta soma yi likis. Yanzun a kira magrib. Insun je gida ya san yanda zaiyi da ita.

*

Da zazzabi ta kwana ruf a jikinta. Dayai maganar suje asibiti ma kuka ta sake saka mishi dole ya hakura ya kyaleta.

Da safe ma shiya tayata har wanka tayi fuskar nan ta kumbura. Shima yai wanka tunda ranar zai tafi.

Saida ya gama shiryawa tsaf tukunna ya dawo inda take kwance.

"Kina so inyi menene?  In tafi inbarki da wannan damuwar?"

Shiru tayi tana kallonshi. Saboda bazai taba fahimtar abinda take ji ba.

Ya ci gaba da fadin.

"Na gaya miki ba jimawa zan ba. Idan na dade sosai sati hudu. Kuma ina da kwanaki da yawa.

Na miki alkawari zan nemo su sofi. Duk inda suka je ni zan nemo su. Ko baki yarda dani bane?"

Da sauri ta dago ta kalle shi. Ta kasa magana. Kawai so take ya mantar da ita ciwon da take ji a zuciyarta ko na awa dayane.

"Please......"

Kawai ta furta tana barin idanuwanta na nuna mishi bukatarta. Lokaci ya kalla. Awa daya da rabi yake da ita kamun jirginsu ya tashi.

Hannunshi ta kamo tana mishi wanni kallo daya batar mishi da tunanin da yake yi.......!"

*

Tun yana wanka yake jinjina kuskuren dayai. Son safiyya ya rufe mishi ido.

Ko da yake babu yanda za.ai ace rabo ya gifta a dai dai lokacin nan. Beside yadai kusa maganin matsalar gabaki daya.

A gurguje ya shirya. Kissing safiyya kawai yayi yana fadin.

"Sai munyi waya. I love you......"

Sannan ya fice daga dakin da sauri. Ajiyar zuciya ta sauke tana lumse idanuwanta........ !

*#TeamAS*

No comments:

Post a Comment