Thursday 4 May 2017

AKAN SO 39

*💘💖AKAN SO💖💘*

~Written by~ :Luβπα Sufyαπ

               39

*Mutane da yawa na fadin sunyi sa.a a rayuwarsu. Nagane hakan lokacin da rayuwa taimun kyautar kanwar da Allah baisa mahaifiya zata bani ba*

*ZAPHIRA ke kyauta ce a gareni daga Allah. Ina miki fatan alkhairi a komai na rayuwarki. Ba saina fadi yanda nake kaunarki ba. Kema kinsani*

*Sorry saboda rashin jina kwaba biyu. Ina busy ne sosai bana samun damar typing sosai. Godiya da kaunarku. ILYA*

*#AnaTare*

Sosai ya riko zee jikinshi.

"Nagode sweetheart. Ban taba zaton zaki fahimce ni ba"

Hawayen daya taru a idanuwanta taji ya zubo. Tasa hannu ta goge su. Muryarta can kasa tace.

"Haba dee. Da zuciya a kirjina fa. Waye zaiki fahimtarka"

Har cikin ranshi lukman yake jinta. Baisan wanne kalar so zainab ke masa ba. Zai iya cewa yafi kowa dace da mata irinta.

****

Zaune yake ya hada kanshi da gwiwa. Bazai ce ga iya abinda yake damun shi ba. Komai ciwo yake mishi.

Tun daga zuciyarshi. Kanshi da koma ina na jikinshi. Yanajin kaman mota tabi takanshi sai dai babu wani ciwo a jikinshi daga waje.

Daga ciki yake jin ciwon. Mikewa yayi. Zaman nan bazai mishi ba. Zaman nan bashi Nana take bukata ba. Tana bukatar yayi setting komai.

Ya roki yafiyar zunubansa datake biya. Dan haka ya mike ya ja iska ya fitar da ita ta bakinshi hadi da ficewa ya kulle dakin yasa key din a aljihun shi.

*

Tun da taxi ta ajiye shi bakin kofar gidansu abinda yai saura daga zuciyarshi yake wani irin dokawa.

Ga wata zufa har cikin tafin hannun shi. Koda maigadi ya bude masa yake tambayarshi wa yake nema.

Kallonshi kawai yai. Ya rasa me zaice. Yau shi ake tambaya wayake nema cikin gidansu. Kalle kalle yake kaman yaune rana ta farko daya taba shigowa gidan.

Komai na nan yanda yasan shi. Wata irin ajiyar zuciya ya sauke yabar maigadin nan tsaye yana binshi da kallo. Da Alama ya mishi kama da yan gidan shisa ya kyale shi.

Da wani nauyi kafafuwanshi ke takawa har suka kaishi cikin gidan. Kaman a lokacin ranar daya bar gidan ya faru haka abin ke masa yawo cikin idanuwa.

Komai na dakin shine banda furnitures. Zai iya rantsewa yana kallon su wani lokaci can baya su duka zaune suna hira.

Wata irin kewar hakan ta saukar mishi. Cikin muryar dabai gane tashi bace yai sallama. Jin shiru ya sake sashi daga murya da sake yin
sallamar.

****

Tunda ta dawo gida ta kasa daina zubda kwalla. Nana ta tsaya mata a rai ba kadan ba. Dakyar ta iya samu ta watsa ruwa.

Haka abbah ya dawo ya sameta. Shima ruwan ya watsa yaci abinci suka zauna falonsu yana kallon tashar Nat geo. Yana kallon abubuwan al.ajabi.

Remote control din dake hannunshi ya ajiye gefe ya fuskanci momma datai nisa cikin tunani. Saida yai magana sau uku bata ji ba ya tabata.

"Meke damunki?"

Cikin sanyin murya tace.

"Baka son jin wannan matsalar nasani"

Da mamaki ya ce.

"Wanne irin magana ne wannan. Abinda yake damunki ai yana damuna ne"

Sauke ajiyar zuciya momma tayi. Cikin nutsuwa ta fada mishi duk abinda yake faruwa. Lumshe idanuwanshi yai yana jin wani irin abu na mishi yawo a zuciya.

Tun ran da fu.ad yasa kafa yabar gidan abin yake manne da zuciyar shi. Bai ya nunawa ne kawai bawai dan baya damun shi ba.

Bacin rai yasa shi yai furucin dayai ba wani abu ba. Bai taba dauka fu.ad zai tafi yaki waiwayarsu ba. Ya dauka abune na karamun lokaci.

Zai gane yayi laifi yazo ya roqi gafararsu komai ya wuce. Ya kasa ko da furta ma momma cewar yana kewar dan nashi kaman yanda take yi.

Yana son sake ganin shi ko sau dayane domin mutuwa ba sallama take ba. Bacin rai duk shi ya hana. Yanzun da take fada mishi maganar Nana har ranshi yake jin dacin abin.

Yasan bakinshi ne ke dawainiya da fu.ad. Fushin daya dauka ne. Hakika fushin iyaye babbar musifa ce ga yayansu.

"Baka ce komai ba"

Momma ta fadi muryarta na rawa. Ya kasa kallonta. Idanuwanshi a kasa yace.

"Ina fu.ad din yanzun?"

Girgiza mishi kai tayi.

"Haneef yace ya sauka a hotel ne. Ban san kowanne ba"

Bude baki abbah yayi zai sake magana suka ji sallama. Saurarawa suka yi. Sallamar suka sake ji wannan karin da dan karfi.

*

Fitowa su momma sukayi tare ita da Abbah dan su dukansu sunji kaman muryar fu.ad din.

In da ya dauka zuciyarshi dokawa take ba komai bane akan yanda yake jinta yanzun. Zai iya cewa su momma dake tsaye suna ganin hakan ta cikin rigarshi.

Hannu yakai wajen ya danna yana kokarin saita zuxiyarshi daga dokawar da take yi. Bakin shi na rawa idanuwanshi kafe kan abbah yace.

"A.... Abbah....."

Kallon shi abbah yake. Ya girma sosai kaman ba fu.ad din shin nan ba. Dan shi daya fi so fiye da kowanne cikin yayanshi ko da baya nunawa.

Yana kallon fu.ad din na takowa zuwa inda yake. Ya kasa cewa komai. Kallon shi yake yana tuna tsahon shekarun da suka wuce bai neme su ba.

Baisan yanda akai kafafuwanshi ke kaishi wajen abbah ba. Zai iya cewa tsantsar kaunar shi da yake yine a zuciyarshi ke janshi.

Saboda a shekarun nan yaki barin zuciyarshi ta fada mishi yanda yai kewar abbah. Yana amfani da fushin da yake yi dashi ne yana danne komai.

Inda Abba yake ya karasa. Hannuwan abbah ya fara kamawa ya sumbata duka biyun. Wani irin abu yake ji yana masa yawo.

Baisan lokacin da kafafuwanshi suka kasa daukar shi ba. Tsugunnawa yai yana sakin hannun abbah. Da duk hannayenshi ya rike kafafuwan abbah.

Duk abinda yake daurewa tun dazun ne yake dawo mishi. Ciwon da yake ji. Dacin da yake ji. Rashin adalcin da rayuwa ke mishi ta kowanne fanni.

Baisan lokacin da hawaye suka fara zubar mishi ba. Kan gwiwoyin shi ya koma ya sake rike kafafuwan abbah dam yana wani irin kuka marar sauti.

Gabaki daya jikinshi rawa yake. Ko ina na jikinshi bari yake. So yake yace abbah ya yafe mishi kalma ko daya taqi fitowa daga bakinshi.

So yake ya fada ma abbah yau yaga wautar daya aikata. So yake ya fada mishi yau yagane amfanin neman shawara. Yagane irin kaunar da suke mishi. Ya gane ba takura mishi suke yi ba.

Ya gane irin wannan ranar suke guje mishi. Yana jin abbah ya tsugunno yana riko shi da nufin ya dago shi daga jikinshi.

Girgiza mishi kai yake. Hawayen harda wanda yaki bari ya zubar lokacin daya tafi yau sun samu hanya.

Dole sai abbah ya tsugunna hannuwan fu.ad ya riko muryarshi dauke da yanayi na tausayawa da kaunar dan nashi yace.

"Fu.ad kai controlling kanka. Saika ce mace. Da karfin hali aka san namiji"

Girgiza kai fu.ad yai. Yana kamo hannuwan abbah yasa fuskar shi a cikin su. Yau lallashi yake bukata. Mahaifin shi yake bukata.

Cikin kuka muryarshi na wani irin sarqewa yake fadin.

"Abbah nagane soyayyarku mai girma ce a gareni. Wallahi nagane duk wata soyayya kasa take data iyaye.

Abbah ka yafemun. Ka yafemun ko zan samu inga dai daina rayuwata......."

Hawaye yaci gaba da zubdawa yana damtse hannayen abbah kaman karamin yaro. Momma dake tsaye itama ta kasa tarbe nata hawayen.

Kallonta fu.ad yai da fuskar shi da harta kumbura.

"Ku yafemun. Dan Allah ku yafemun....."

Muryar abbah na rawa yace.

"Na yafe maka fu.ad. Na yafe maka duniya da lahira"

Wani irin sanyi yake ji yana ratsa shi na daban. Momma ya kalla. Kai kawai take iya daga mishi alamar itama ta yafe mishi. Ta dade da yafe mishi.

Kallon abbah yai sosai. Idanuwanshi na sake cika da da wasu hawayen.

"Abbah mutuwa zatai. Nana zata mutu. Abbah ku taimakamun ita kadai nake da a duniya.

Nayi wautar da in ta tafi bazan sake sanin meye dadin da ya kalleka cike da kauna a idanuwanshi ba.

Bazan sake sanin.......abbah"

Kasa karasawa yai yanda yakejin numfashin shi har wani sama sama yake yi. Dakyar abbah ya kamashi yaja shi kan kujera ya zaunar dashi.

Nasiha ya shiga yi mishi da nuna mishi girman yadda da kaddara a musulunce. Jikin fu.ad ya kara yin sanyi.

Momma ta kawo mishi ruwa ya sha. Suna nan zaune aka kira magrib. Bangaren abbah fu.ad din yabi shi sukai alwala suka fita masallaci tare.

*

Tare suka ci abinci a plate daya. Sai dai duk wani motsi da fu.ad zai saiya sake kallon abbah yace.

"Abbah ka yafemun"

Saida ya gaji yace mishi.

"Fu.ad komai ya wuce. Anan zaka kwana yau. Gobe kaje ka kwaso kayanka ka dawo gida...."

Kai ya jinjina ma abbah alamar yaji. Wata irin girmamawa ta daban yake jin yana musu. Wata irin kauna daya san ko rabin wadda suke mishi bata kai ba.

Wanda ya haihu yasan meye dane kawai zai iya sanin girman kauna har haka.

Har sukaje sallar isha.i da abbah suka dawo. Dakin shi tun nada momma ta bashi mukullin ya wuce.

Yai mamakin ganin dakin fes. Komai na nan babu abinda aka canza. Wani irin abu yaji na daban na masa yawo.

Duk wanda ya dauki soyayyar iyaye abin wasa hakika yana daya daga cikin marassa rabo.

Kwanciya yai yanajin sanannen yanayin dake cikin dakin na nutsar dashi. Yau zai huta. Yau zaiyi jinyar ciwukanshi. Zai tattara duk wani strength daya san Nana na bukata daga wajen shi.

****

Tunda ta tashi ta zabi kayan Nana data san tafi so. Wata doguwar riga ce ta atamfa purple.

Ta dauko mata takalmanta da hijab purple. Dan sunyi da yusra zata zo karfe goma na safiyar ranar dan suyi magana da Nana.

Kitchen take tana soya kwai nana ta shigo. Sanye take da riga da wanda kanta da hula. Duk ramar datai bai hana safiyya ganin tayi mata wani irin kyau daya taba mata zuciya ba.

Kujera ta janyo ta hau sama. Safiyya ta lumshe idanuwa.

"Nana na hanaki tsayuwa kan kujerar nan. Sai kin fado ko?"

Dariya tai tana leqa frying pan din da safiyyar ke soya kwai hadi da fadin.

"Na tsaya da kyau bazan fado ba. Mumy in tambayeki?"

Saida ta juya wainar kwan dake ciki sannan ta amsa da.

"Uhum ina jinki"

Shiru tadanyi na wani lokaci.

"Kinyi alkawari ba zakiyi kuka ba in na tambaya?"

Wani miyau safiyya ta hadiye dan tun kamun ma ta tambaya din taji hawaye na taruwa a idanuwanta. Muryarta a sarqe tace.

"Ina jinki"

"Menene soyayya? Ya ake ji in ana soyayya?"

Cike da mamaki safiyya tace.

"Me yasa kike tambaya?"

"Oh oh mumy. Karki yi kuka please idan na fada miki"

Jinjina mata kai tayi. Idanuwa nana ta ware kan fuskarta hadi da fadin.

"Saboda nasan bazan girman da zansan ya akeji ba shisa nake so ki fadamun"

Abun dake tsaye wuyanta take ta so ta hadiye ta kasa. Dan gyaran murya tai tana kifta idanuwanta cikin son maida hawayen dake son zubo mata.

Kettle ta dauko ta dora musu ruwan zafi sannan ta fuskanci Nana tace.

"Soyayya wani abune mai girma Nana. Babu kalaman da zaka dora girmanta akai. Wani irin yanayi ne na daban"

A nutse Nana ke kallonta tana son fahimtar me take fada. Kamun taci gaba da cewa.

"Lokacin da kake son wani zakaji zuciyarka ta cika. Bata gane komai sai wannan yanayin.

Zakaji kaman daman can an halitta maka zuciyarka ne domin mutum dayan nan"

Tunawa take. Tana tuna yanda taji son fu.ad. Yanayin soyayyar shi a zuciyarta. Komai dawo mata yake da wani irin bazata.

"Haka kikaji da dady?"

Nana ta tambaya muryarta da murmushi. Hararta safiyya tayi. Shagwabe fuska nana tayi.

"Mumy please. Waye zai fadamun in bake ba?"

Yar dariya safiyya tayi. Karya itace karshen abinda zata so taima Nana a wannan lokacin. Dan haka ta zabi ta gaya mata gaskiya.

"Ya girmi hakan da dad dinki"

Cike da jin dadi Nana tace.

"Har yanzun?"

Wannan tambaya ce da bata son amsa ma kanta ita. Bata son ta fara wannan tunanin ko da wasa. Da wani rauni ta kalli Nana hakan yasata fadin.

"I'm sorry"

Murmushi tayi.

"Daukar mana wannan kikai mana falo gani nan zuwa"

Ba musu Nana ta dauki plate din dankali da na wainar kwan ta wuce. Sauke numfashin da take rike dashi tayi.

*

Suna gama breakfast din Nana tace zataje ta kara yin wanka. Itama safiyyar wankan taje tayi.

Tana fitowa yusra ta kirata suka gaisa. Tace mata zata iya tahowa a shirye suke. Atamfa ta saka daviva ruwan hoda ta matukar amsar jikinta.

Duk da babu wata kwalliya a fuskarta. Tana zuwa falo ta zauna Nana ta fito sanye da doguwar rigar daya fito mata da ita da er hijab.

Kallonta safiyya take. Harda jan baki pink a lebenta. Dan murmushi tayi.

"Bana so inyi kama da marassa lafiya. Bana son mutane su kalle ni da irin abinda nake gani cikin idanuwanku bayan basu sanni ba"

Sauke idanuwanta tai daga kallon da take ma Nana a sanyaye tace

"Wanne irin kallo ne muke miki Nana?"

Karasowa tai kusa da safiyya ta zauna.

"Tausayi. Sona duka a tare. Inkun mun bana jin kaman banida lafiya. Amman in anty jana tamun banajin dadi.

Bana son ganin shi a idon kowa sai naku"

Sauke ajiyar zuciya safiyya tayi tai shiru saboda bata san me zata ce ba. Wasu maganganun idan Nana tayi sai su saka rasa naka kalaman.

****

Da motar abbah yaje hotel din ya dauko komai nashi yai Check out ya dawo. A gida yai wanka sukai breakfast gabaki daya.

Wata irin kewar Nana yake ji. So yake kawai yaje ya ganta. Shiya fara mikewa daga kan dining din hadi da fadin.

"Momma aramun motarki"

Kamun ta amsa Abbah yace.

"Ka dauki mota daya cikin nawa kawai"

Saida ya kalli abbah sosai sannan yace.

"Nagode abbah. Allah ya kara girma"

"Amin. Kaje daki mukullan suna nan gefen gadona"

Kai yadan daga alamar to. Haryazo wucewa abbah yace.

"Fu.ad......"

Dawowa yai ya zauna. Yana bama abbah dukkan hankalin shi.

"Ka kawomun ita anjima inganta"

Cike da kaunar abbah cikin idanuwanshi yace.

"In shaa Allah"

Sannan ya mike. 406 ya dauka dan shi yanzun duk wani kyale kyalen duniya ya fice mishi a rai.

Daya shiga ciki yaja motar wani murmushi ya kwace mishi. Rayuwa ba komai bace ba. Wai yau shine kwata kwata bai damu da mota ba.

Ta zame mishi wani abu dazai hau ya biya bukatarshi. Bai kuma damu ba. Abin ya bashi mamaki.

Cike da tunani barkatai yahau titi.

****

Kwankwasa kofa sukaji suna zaune suna hira ita da Nana. Ware idanuwa Nana tai kan safiyya.

"Turo"

Safiyya ta fadi. Dan ta dauka yusra ce. Fu.ad ne ga mamakinta. Kallon shi take.

Sanye yake da jeans blue. Sai wata hoodie fara kal. Hular na kanshi. Yaja hannun hoodie din zuwa gwiwar hannun shi.

Yai wani irin kyau. Sallama yai. Ta amsa a sanyaye saboda hakan take jin jikinta ya mata wani irin sanyi.

Da gudu Nana ta tashi taje ta rukunkume fu.ad tana fadin.

"Dady. Inata missing dinka"

Dagota yai jikinshi. Ya sumbaci kuncinta duka biyun sannan yace.

"Princess ta sha kyau yau. Inata missing dinki nima"

Wayarshi ya lalubo cikin aljihunshi da dayan hannun. Dayan na rike da Nana dake faman murmushi bakinta yaki rufuwa.

Camera din ya bude ya daga ya dauke su. Sake rike shi nana tayi yana ta daukarsu.

Sumbatarta yai a kunci yana daukar su a haka. Hannunshi mai wayar yasa yana nuna mata alamar tai kissing dinshi a kumatu.

"Dady zan shafa maka lipstick"

Daquna fuska yai dake nuna bai damu ba hadi da juya mata idanuwanshi. Dariya tayi.

Ta zagaya hannayenta duka biyun a wuyanshi sannan ta sumbaci kumatunshi ya dauke su wajen kala goma. Sannan ya kalli safiyya.

Saurin kauda kai tayi. Dan ta fahimta sarai. Babu abinda zai ja mata daukar hoto dashi. Nana ya kalla yana wani matse lips waje daya.

"Mumy please kizo muyi"

Ta fadi. Ware mata idanuwa safiyya tayi alamar bata so. Nana tace.

"Dady zaka dauki pic da mumy"

"Banda matsala princess. Duk abinda kike so"

Fu.ad ya fadi yana karasa maganar da kallon safiyya. Harara ta watsa mishi wato itace take da matsala.

Mikewa tai. Sai lokacin ya samu damar kallonta sosai. Numfashin shi yaji yana masa wasa wajen fita da komawa.

Ta canza in all the good ways. Kyanta ya fito fiye da da. Kallon da yake mata yasa ta tuna babu mayafi a jikinta. Kallon shi tai taga idanuwan nana basa kanta.

Yanda iya shi kadai zai gani ya fahimta tace

"Bana son kallo"

Daga mata gira yai duka biyun. Ta taka ta karasa inda yake. Duk da bayanshi ta tsaya bai hana kamshin da take ya cika mishi hanci ba.

Mamaki yake sosai saboda collection din smart din daya daina amfani dasu ne saboda suna tuna mishi ita. Shine a jikinta.

Sake baza hanci yai kamshin na tuna masa abubuwa da yawa. Dakyar ya iya daga camera din ya dauke su kala biyu duka safiyya na bayanshi ta wani hade fuska.

Zai dauki na ukkun aka kwankwasa kofar. Tasan wannan karin yusra ce. Da kanta taje ta bude kofar. Aikam yusra ce sanye da doguwar riga fara. Tai rolling farin mayafi. Hannunta dauke da wata jaka.

Da fara.a suka gaisa da safiyya ta shigo ciki. Gaishe da fu.ad tayi ya amsa a dakile.  Saida ta zauna sannan tai ma Nana murmushi hadi da fadin.

"Nana"

Murmushin Nana ta mayar mata.

"Ina kwana"

Ta fadi yusra ta amsa. Yarinyar ta mata kyau. Basai an fada mata ba tasan mutumin dake rike da ita shine babanta. Dan ga kamanni nan.

"Gata tazo Nana"

Fu.ad Nana ta kalla.

"Dady sauke ni"

Kallonta yai yace.

"Wacece?"

"Yar jarida"

Lokaci daya idanuwanshi sukai wani irin haske. Sake rike nana yai gam. Baya son yarshi a TV balle duniya ta kalle masa yarinya.

Baya son labarinshi a kunnuwan kowa. Baya son duniya ta kalle shi da matsayin uban daya kasa yima yar shi komai. Saida yaji Nana nason sauka da kanta sannan ya ajiyeta.

Yusra ya kalla.

"Bana son ki dauki komai nata....."

Ya maida hankalinshi kan safiyya

"Ina son magana dake"

A dake tace.

"Seriously fu.ad? Kabari mugama tukunna"

Kara bata mishi rai take

"Ki taso ku muyi a gabanta"

Mikewa tai. Kitchen ya nufa tsabar masifa ce fal a cikinshi. Abin yaso ya bata dariya.

Suna karasawa tace.

"Saika cemun yunwa kakeji drama king"

Dariya tayi saboda yanda yake mata kallon rashin fahimta. Lokaci daya yaji ya sake kulewa. Ya ma zama wani game wajenta.

"kitchen ka kawo mu. Me kake tunanin zan dauka?"

Sai lokacin ya kulla. Yadan dakuna fuska dan ya kasa ganin abin dariya cikin lamarin.

"Bana son yarinyata a TV. Bana son kowa ya kalleta da kalar me zai fada.

Saboda me ma zaki kirasu?"

Hannunta ta dora kan kugu tana kallon ikon Allah.

"Na dauka tun a asibiti na fada maka tana son magana dasu. Kace bakomai"

Kallonta yake dake fassara ashe baki da hankali?

"Na dauka kingane dan a gabanta ne. Bakiga idanuwana ba?"

Yar dariya tai cike da takaici.

"Ka fada mata da kanka"

"Bana son ince kar tayi abinda take so"

Ya fadi. Bata san randa fu.ad zai bar son kanshi ba. Bata ga rana ba. Shi bashida zuciyar dazai ce ma Nana aa sai ita kenan.

Kaman daga sama suka ji ance.

"Dady"

Da sauri suka kalli Nana a tare. Idanuwanta kan fu.ad a kafe tace.

"Na hakura tunda baka so"

Tsugunnawa yai. Ya sa hannu ya tallabi fuskar Nana cikin hannuwanshi.

"Princess bana son maganganun mutane ne. Bana son ki zama abin kallo da magana.

Bana son kowa ya miki kallon something weak and fragile. You are my daughter Nana.

Zuciyata ba zata iya dauka ba"

Tallaban hannuwanshi dake fuskarta tayi da nata. Murmushi tai mishi.

"Ba saika mun bayani ba. Bansan me yasa nake son magana da ita ba. Na hakura tunda baka so"

Sunbatar goshinta yayi.

"Thank you princess"

Dariya tai mishi.

"Kubarni in fada mata da kaina"

Kamun suce wani abu da gudu ta fice daga kitchen din. Suka kalli juna shida safiyya suna sauke numfashi a tare.

*

Zama tai gefen yusra.

"Anty bazan yi ba. Dady baya so. Na hakura. Amman ki tambayeni ko me kike so zan amsa miki indai ba zaki saka a TV ba"

Murmushi yusra tayi mata. Duk yanda take son tasa labarin yarinyar nan baikai yanda ta fahimci babanta ba. Ko itace ba zata so yarta a TV ba sam.

Hira suka danyi kadan da yusra. Tana tambayarta ya akai taga babanta duk ta amsa ta. Rokon Nana tayi sukai hoto tare.

Sannan ta mike ta kalli su fu.ad dake bayansu.

"Nagode sosai. Allah ya bata lafiya"

Suka amsa da amin. Har kofa safiyya ta rakata sannan ta dawo. Fu.ad baice mata komai ba. Wajen Nana yaje ya zauna.

"Zan je unguwa. Idan na dawo zamuje tare dake okay?"

Kai ta daga hadi da fadin.

"A dawo lafiya. Love you"

Wani kumburi zuciyarshi tayi. Saida yai hugging Nana yanajin kaman ya mayar da ita cikinshi kar wani abu ya sameta sannan ya ce.

"Love you more"

Dariyar nan da yake so tai mishi cikin kunnuwanshi sannan ya saketa. Mikewa yai ya sauke idanuwanshi kan safiyya.

Wani irin kallo yake ma safiyya data kasa fahimtarshi. Muryarshi ya saukar sosai. Idanuwanshi na cikin nata yace.

"Zan dai dai ta komai. Zan cika miki wannan alkawarin"

Lumshe idanuwanta tayi. Tana jin yanda yake fama mata tsofin ciwukanta. Hular rigarshi ya cire daga kanshi ya kalli Nana yai mata murmushi sannan ya nufi hanyar kofa.

*

Yana fita daga gidan lukman na kiranshi a waya. Dagawa yai hadi da fadin.

"Lukman....."

"Fu.ad ya ne? Ya nana?"

Saida yai jim ya amsa da.

"Okay i guess"

Yanajin yanda lukman ya sauke numfashi kamun yace.

"Kana gidan ne?"

Girgiza kai yai kaman yana ganin shi.

"Ina hanyar bichi. Bankai da fita daga cikin gari ba tukunna dai. Em' gonna make it right. Duk abinda na bata"

"About time fu.ad. Daka fadamun da munje tare"

Murmushi yai. Har ranshi yaji dadin maganar lukman din sai dai wannan abune da zaiyi shi kadai. Baya son kowa ya tayashi.

Yagaji da yanda tun yarinta lukman da haneef ke share hanyar daya bata. Wannan karin zaiyi komai. Laifin shine shi kadai kuma shi kadai zai gyara.

"Nagode lukman. Nagode fiye da yanda zan iya fada. Kuskure na ne. Ina son gyarawa da kaina."

"Hmm. Be safe. Just be safe fu.ad"

Yar dariya yai.

"Yeah whatever. Ka shafamun kan junior......"

Sai yanzun ya tuna. Yadan daki steering motar hadi da fadin.

"Em such a bad uncle. Nama junior alkawari lukman ko ka tunamun"

Dariya kawai lukman yai ya kashe wayar. Ajiyeta yai gefe ya mayar da hankalin shi sosai kan tukin da yake yi.

Daya dawo anjima zai cika alkawarin nan.

****

Tura dakin ikram yai da sallama. Tana kwance kan gadon ta tana karatun Qur.an. Saida takai ayar sannan ta amsa shi.

Qur.an din hannunta ta rufe ta ajiye gefe a hankali. Da dan murmushi tace.

"Pa?"

Dan tasan ta musu saida safe tun kamun isha.i. Bakuma al.adarshi bane shigowa dakinta babu wani dalili.

Gefen gadon ya zauna. Yana rasa ta inda zai fara.

"Lafiya dai ko? Ina mumy?"

Ganin yanda duk ta rikice yasa shi saurin cewa.

"Komai lafiya ikram. Kawai ina son magana dake ne"

Gyara zama tayi kan gadon.

"Alright. Ina ji"

Saida ya sauke numfashi sannan yace.

"Zan kara aure ikram. An sa rana yau. Nan da wata biyu"

Shiru tayi tana kara tauna maganar shi na tsayin mintina biyar kamun tace.

"Why?"

Tana tsare shi da idanuwa. Dan daga kafadar shi yai.

"Just......"

"Kana son mumy?"

Kai ya daga mata. Dan tana jin tsoro. Taga yanda kishiyar maman kawarta jawahir take basu wahala. In tana bata labari takan gode ma Allah da babansu bai kara mata ba.

Sosai ta kalle shi. Tsoro cike fal da idanuwanta. Hannunta ya kamo. Yana son ya fara zame ma yayanshi aboki da zasu iya magana ba tare da shakka ba.

"Kinsan zaki iya fadamun komai ko? I am your dad. Your best friend ikram"

Kai ta jinjina.

"Kawai ina jin tsoro. I love mum sosai. Kaima haka. What if ta kwace mana kai"

Da wani irin yanayi yace.

"Babu wanda zai kwace muku ni in shaa Allah. Babu abinda zai canza. You will be there for me dake da mum inki dasu umar.

Ba zaku bari kowa ya kwace ni ba.?"

Fuskarta babu wasa tace.

"Sosai ma. Promise komai bazai canza ba?"

Saida yai jim sannan yace.

"In shaa Allah. Kumin addu.a Allah ya tabbar mun da alkhairi. Shi nake bukata"

Sai lokacin tai mishi murmushi. Yasan da wuya ta sake cewa wani abu. Ikram bamai yawan magana bace ba.

Har yakai kofa tace.

"Pa....."

Ya juyo ya kalleta.

"Thank you"

Murmushi jabir yayi. Ya jinjina mata kai kawai ya fita yana ja mata kofar. Numfashi ya sauke yana juya idanuwanshi.

"So awkward...."

Ya fadi kasa kasa. Ya na takawa zuwa dakin su. Jana ya samu inda yabarta tana dudduba wasu takardu.

Idanuwanshi taji suna mata yawo ta dago ta kalle shi sai raba idanuwa yake. Dariya ya bata.

"Ya dai?"

Dan rausayar dakai yayi.

"Kin banni da ikram ni kadai ko?"

Dariya ta sake yi.

"Baga shi harka gama ba. Nace maka ba wani wahala"

Karasawa yai ya zauna kusa da ita. Takardun dake hannunta ya karba ya ajiye gefe daya.

"Lokaci na ne yanzun. A taimakamun a ajiye office work din nan jana"

Shagwabe fuska tayi.

"Nabar ma ayna ai"

Ware idanuwa yai.

"Tun yanzun?"

Dan murmushi tai cike da kishi. Har daci take ji a wuyanta. Ya karance ta tsafa dan haka ya matsa daf da ita sosai.

"Naki ne ni jana. Kinsan wannan ko?"

Daga mishi kai ta iya yi. Duk soyayyar nan a kwanaki sittin da wata zata dinga rabata. Addu.ar ta ci gaba dayi a zuciyarta.

Saida taji wata nutsuwa ta saukar mata sannan ta fara nuna ma jabir kalar soyayyar da take mishi......!

****

Kanshi tsaye gidan su safiyya ya wuce da wani irin yanayi na nasara da yake saka shi murmushi shi kadai.

Da sallama ya shiga. Nana na zaune tana kallon cartoon network. Ta ruga tqna mishi sannu da zuwa.

Safiyya ta fito daga daki.

"Sannu da dawowa"

Ta fadi. Kai yadan daga mata. Yana kallonta hadi dayin murmushi. Komai nasu ya kusan gyaruwa. Zai bata mamaki bada jimawa ba.

"Zamu fita da Nana"

Ya fadi. Kai ta daga mishi. Da gudu nana ta ruga daki ta dauko hijab dinta da takalmi ta dawo.

Safiyya tace.

"Nana ko goodbye?"

Da sauri tana dariya ta karasa wajen safiyya ta rungumeta. Sakinta tai ta juya tana fadin.

"Sai mun dawo"

"Allah ya tsare hanya"

Safiyya ta fadi. Fu.ad ya kamq hannun nana cikin nashi suka fita. Wata ajiyar zuciya ta sauke gidan na mata wani irin shiru.

*

Yana tuqi ne nana tace.

"Dady in rokeka?"

Kai ya daga mata. Dan bayajin akwai abinda zata nema indai zai iya dazai kasa yi mata.

"Ka auri mumy. Dan Allah ku koma aurenku!"

Wani shiru yaji cikin kanshi. Zuciyarshi na tsayuwar wucin gadi kamun ta ci gaba da aiki.

"Please. Tana bukatarka in bana nan. Kana bukatarta in bana nan. Tana sonka sosai. Dan Allah karka ce No"

Zufa ke keto mishi ta ko ina. Nana na tambayarshi abu mai girma. Tana tambayarshi abinda bayajin zai iya.

Bashida abinda zai ba safiyya. Bashi da farin cikin da take bukata. Parking yai gefe yana maida numfashi.

"Nana...."

Ya kira sunanta yana rasa me zai ce. Ta ina zai fara fada mata sakin safiyya dayai yanci ne ya bata. Farin cikin daba zai iya bata vane ya barta ta samu da wani.

Idanuwan nana cike da hawaye tace.

"Ka daina sonta ko?"

Da sauri ya girgiza kanshi. Son da yake ma safiyya bazai taba misaltuwa ba. Sonta yasa yabarta. *Akan so*n da yake mata ya zabi ya barta inhar zata samu farin cikin da shi bazai iya bata ba.

Hawayen da suka zubo mata tasa hannu ta goge. Tana son tagansu sun koma. Tana son hakan fiye da yanda take son lafiyarta.

"Please dady. Bana so inbar mumy ita kadai. Bana so...... Bata da kowa......"

Kuka Nana take yi. Jinshi yake har cikin tsokarshi. Kamo Nana yayi yana tallabar fuskarta yana goge mata hawayenta da sauri.

Dan shi kanshi da zai samu wanda zaima kuka yi zaiyi.

"Ina sonta Nana..... I love your mum. Ita kadai zan so har abada....."

Cikin kuka nana tace.

"To ka aureta"

Cikin rasa yanda zai ce ma Nana yasa shi fadin.

"Banda abinda zan bata. Banda komai dazan bata"

Rike hannuwanshi Nana tayi.

"In tana sonka a haka fa? Zaka aure ta?"

Kai ya daga ma Nana. Son da yake ma safiyya mai girma ne. Yasan bata son shi ta tsane shi yanzun. Ta kuma kara tunda bashida abinda zai bata.

Yaji dadi saboda zai bata mamaki zuwa gobe da safe in shaa Allah. Zai bata abinda yasan tana so. Abinda yai mata sanadin salwantarshi.

"Zan ma mumy magana. Kaji"

Kai ya daga mata. Ya goge mata fuska hadi da fadin.

"Bana son kukanki. In kuma na sake gani zan fasa"

Da sauri tasa hannu ta sake goge fuskarta.

"Na daina. Kayi hakuri bazan sake ba"

Murmushi yai.

"Good girl..... Zauna sosai to"

Gyara zamanta tai ya tayar da motar suna tafiya..........!

*#TeamAS*

No comments:

Post a Comment