Tuesday 23 May 2017

AKAN SO 49

*💘💖AKAN SO💖💘*

~Written by~ :Luβπα Sufyαπ

www.Loobnerh.blogspot.com

Wattpad: LubnaSufyan

               49

*Abubuwa da yawa suna faruwa damu a rayuwa. Na bakin ciki. Na farin ciki. Sai dai a cikin kowannensu idan muka duba akwai darasi*

*Zumunci na da girma. Wasu lokutan zumuncin dake tsakaninka da wanda baka hada jini dashi ba yana kaiwa mataki babba*

*In zaka yarda karka yarda da yawa. Karka daga burinka akan komai. Ka yarda da Allah. Ka muka burikanka a wajen Allah. Sauran zasu zo da sauki*

*Allah ya nuna mana Ramadan lafiya*

*Farida Aminu.(A duk lokacin dazan kwanta da dare inda zan iya ganin yanda taurari suka tsaru muryark nakeji anty farida. "Baby ki kalli yanda Allah Yai ma sama ado da taurari masu kyau. Hikimomi na Ubangiji yawa ne dasu.)*

*She was so sick. Ban taba ganin kalarki ba. Nakan tunaki da hawaye. Saidai girman murmushin saninki yakan rinjayi hawayen*

*Auwal Aliyu.(Nai kuka. Nai kuka uncle auwal. Sai da baka nan nagane muhimmanci zumunci. Mutuwarka tazomun da darasi na fahimtar gaggawa cikin ziyara a duk lokacin dana samu dama*

*Dalilai da yawa basu sa nasanka ba. Hakan bai hanani kewarka ta yanayin da bazai fadu ba. I wish and wish......*

*Adam Abdullahi Gambo. (You raised me. Kana nan lokacin dana fara tafiya. Lokacin dana bude bakina. Lokacin dana dora tukunya danyin girkina na farko. A tare dakai nasan menene rayuwa. A tare dakai nasan menene hakuri. A taka rayuwar na samu shafukan nawa)*

*Ba kakana bane kawai kai. Babana ne. Mamana ne. Yayata. Yayana. Abokina. Abokiyata. Alhamdulillah dana sanka a rayuwata*

*Ummiee (Har yau idan wani ya kira LUBA da muryarki sunan yake karasowa kunnuwana)*

*Me zance? Me zan fada akanki ummie? Ina kalaman suke? Ina kaunarki yayi kadan wallahi. Nayi kewarki bai isa ba*

*Uncle sulaiman (Kewarka na damuna idan na duba abubuwa da dama. Ya Allah. Ban taba ganin fuskarka da wani abu daya wuce fara.a ba.)*

*Allah ya jikanku. Allah ya sadaku da Rahmarshi. Allah ya haskaka kabarinku. Allah ya hadamu a aljanna in gaya muku kalar kaunar ku da nake daban samu na fada muku ba*

*Wannan ba bankwana bane. Wannan yana nufin sai na taho*

*SA.ADATU HABEEB (May Allah ease your pain and suffering. May Allah make your departure an easy one)*

*I..... I feel your pain? Scratch that. I will never know what you are going through. It just hurt a lot (Allah kaine abin godiya a kowanne hali)

*#AnaTare*

*Saura epilogue in shaa Allah*

*BAYAN SHEKARA DAYA*

Wani irin zama su jana suke mai natsuwa. Duk da wata doguwar hira bata hadata da ayna.

Yara dai tunda ita tama fita zama dasu. Wani lokaci ma ko tana gidan ayna ke kula dasu. Hakan bai dameta ba.

Tadai saka idanuwa ne saboda taga ko yanayin tarbiyar da ta dora yaranta akai ya sake. Ga mamakinta sai dai ya karu.

Kananan abubuwan da bata tsayawa ta kula ko ma tace bata da lokacin kula dashi ayna na tsaya mata akan hakan.

Yau ma kaman kullum ta gama shirinta tsaf da yake dakinta jabir yake kuma yama rigata shiryawa tare zasu fita.

"Jana sai mun latti ko?"

Ya tambaya yana sake duba agogon dake hannunshi. Da murmushi a fuskarta tace.

"Ka tafi inka gaji da jira"

"Zaki hau napep kenan?"

Ya bukata yana tabbatar da idanuwanshi sun sauka cikin nata kamun yai tambayar. Yana kallon yanda take wani matse labba yasan tsokana ce fal cikinta.

"Kadai hau napep honey j"

Dafe kirji yayi.

"Yes. Ka manta motata ce? Inkuma ayna zata ara maka tata ne to kaje ka amso"

Rausayar dakai yai gefe

"Allah ya horemun in sake siyan wata motar yanda in dayar ta samu matsala ba sai an mun goriba"

Dariya jana tayi sosai.

"Amin. Ko in ara maka? Ka siya inka samu ka biyani"

Karasawa yayi inda take ya zagaya hannuwanshi zai rungumeta ta mike da sauri.

"Nagama shiryawa"

Girgiza mata kai yake alamar bai yarda ba.

"Zo nan kiga in tayaki"

Pillow ta dauka kan gadon ta jefa mishi tana daukar jakarta. Ya rike yana dariya.

Tare suka fita. Jana ta tsaya a falon ya wuce bangaren ayna ya fada mata sun wuce. Bata daukarma kanta gulmar yima ayna sallama ba dan zata tafi work.

Tana danne abubuwa da yawa. Saidai bata takura kanta ba. Shi dai da yake wajibi akanshi yayi. Sai dai ayna ta burgeta yanda kullum ko da jabir na dakinta saita zo da kanta sun sallama da janar.

Fitowa yayi ya ce ma jana.

"Bata da lafiya. Zazzabi ne ruf jikinta"

"Subahanallah......"

Jana ta karasa tana ture jabir din ta wuce dakin ayna din. Karo na farko sa kafafuwanta suka taba taka bedroom din ayna a shekara daya datai a gidan.

Koma tace bangarenta gabaki daya. Sai dai insun hadu a babban falo sannan. Sosai ta dudduba  ayna.

Sannan ta taimaka mata ta tashi daga kan gadon. Take fadama jabir sai sunje asibiti dole. Bai musa ba ya bata mukullin motarta ya dauki na ayna din.

*

Abinda jana take zato ne. Ta lumshe idanuwanta tana danne wani kishi da take jin ya taso mata.

Wayarta ta dauko ta kira jabir. Ringing din farko ya daga.

"Albishirinka amman saika bani goro"

Tana jin murmushin da yake cikin muryarshi.

"Saikin zabi kalar goron da kike so. I promise"

Yar dariya tayi.

"Ayna nada shigar ciki sati hudu"

Tana jin yanda yaja numfashi hadi da fitar dashi kamun addu.o.i su biyo baya. Sosai ta rintse idanuwanta.

Hakan dayai ba bakon abu bane saboda itama yayi duk cikin yaransu. Ta rasa ko menene na jin kishi a ciki.

"Thank you jana. I love you. Ki zabi goronki"

Saida tadan yi jim tana son danne abinda take ji kamun tace.

"Sai nayi tunani tukunna. Barin fada musu ina da patient mu koma gida.

Babu dadi in kaita in barta ita kadai"

"You don't have to do this jana. Atika na nan ai"

Girgiza kai tayi.

"Badon kai nayi ba. Ko ni. Nayi saboda karamcin da ke tsakanin su da yarana."

Shiru jabir yadanyi kamun yai mata sallama.

*

Kaman yanda ta fada hakan tayi kuwa. Har daki ta raka ayna ta tambayeta ko tana bukatar wani abun tace mata aa.

Sosai tai mata godiya. Murmushi kawai tayi ta fada mata tana dakinta indai tana bukatar wani abu ko flashing tai mata sannan ta fice.

Gyara kwanciya ayna tayi. Jana mutuniyar arziqi ce. Bakowa ne zai dace da kishiya irinta ba.

****

Zaune suke tana yanke ma farhan farce. Sukaji sallama da sauri ta saki kafarshi ta mike tana amsawa.

A fadace yace.

"Nuriyya ki daina saurin mikewa haka. Saikin jika baby na ciwo ne ke kam?"

Dariya tayi tana mamakin farhan. Cikin da bai wuce sati uku ba ko motsin kirki bata da ikon yi sai yayi fada.

Sosai fara.arta ta karu ganin anty maimuna.

"Anty maimuna. Sannu da zuwa"

Nuriyya ta fadi.

"Ki kara so mana"

Da fara.a a fuskar anty maimuna ta karaso dakin. Farhan ya kalleta yana murmushi.

"Anty maimuna. Ina wuni"

Saida ta samu waje ta zauna sannan tace mishi.

"Lafiya kalau farhan. Ya mai jiki?"

Ya amsa da

"Ta warware sosai anty. Muna cewa mu samu lokaci mu shigo mu gaishe daku"

Zuwan nuriyya ya katse musu hirar. Lemo da cup ta ajiye ma anty maimuna a kasa. Ta na samun waje gefe ta zauna.

"Aikam dakin bar drink din nan. Daga gida nan nayo fa. Ya jiki?"

Murmushi nuriyya tai a kunyace.

"Naji sauki"

"Allah ya kara sauki ya raba lafiya"

Farhan dake zaune kan kujera ya amsa da.

"Amin thumma amin"

Zungurinshi nuriyya tayi tana mamakin rashin kunya irin ta farhan. Anty maimuna kanwar babanshi ce uwa daya uba daya.

Mikewa anty maimuna tayi.

"Bara kuga inzo in wuce. Nan har gidan hajja zanje"

"Anty wannan irin zuwa da wuri haka?"

Cewar farhan. Nuriyya ta karbe da fadin.

"Wallahi kuwa. Daga zuwa sai tafiya"

Dariya anty maimuna tayi.

"Daman jikinki nazo dubawa. Zumunci ai yanzun aka fara in banda abinku.

Duk ana tare"

Har kofa suka rakata suna shigowa nuriyya tasa kafadarta ta ture shi.

"Kai ko? Harda cewa amin. Kasa inata jin kunya"

Dariya sosai farhan yayi.

"Jimun ke please. An mana addu.a me kyau bazan amsa ba?"

Turo baki tayi tana dakuna mishi fuska. Hannuwanta ya kamo yana janta jikinshi.

"Me nace kan turo bakin nan a gabana?"

Kanta ta boye a kirjinshi tana dariya. Rungumeta yai tsam a jikinshi yana jin duminta.

Yana godema Allah daya tsara mishi rayuwarshi da ita a cikinta. Yana kuma sake gode Ma Allah da yasa ya bi shawarar nuriyya ya nemi dangin babanshi.

Laifin babanshi mai girma ne a gare shi. Waya sani wata rana ya iya yafe mishi. Ba zaka taba fadar me zai faru dakai ba a rayuwarka.

Sosai ya sake matse nuriyya a jikinshi. Kasa kasa tace mishi.

"Idan mace muka haifa sunan ta farhana in shaa Allah"

Murmushi yayi.

"Idan namiji ne sunanshi nawaf"

Dago wa tai daga jikinshi hawaye ba taruwa a idanuwanta. Wasu irin emotions na mata yawo.

"Da gaske? You will name him that?"

Kai ya daga mata yana sa hannu ya tallabi fuskarta.

"Da gaske sunanshi nawaf. Indai muka haifi namiji ko ba wannan cikin ba"

Sumbatarshi tai tana nuna mishi godiyarta. Kamun ta kwantar da kanta a kirjinshi.

"I love you. Thank you"

"I love you more. Allah ya jikan nawaf"

Ta amsa da.

"Amin. Allah ya jikanmu muma. Munfi nawaf bukatar wannnan addu.ar saboda karshen shi yayi kyau.

Namune abin tsoro"

"Shhhhhhhhh. Zaki kashemun jiki"

Farhan ya fadi. Dan maganganunta sun tsorata shi lokaci daya. Kuma sun shige shi. Dariya nuriyya tayi.

"Idan jikinmu yana sanyi lokaci lokaci kilan yasamu shiryama mutuwarmu kamun ta same mu"

Sauke numfashi yai. Yai shiru yana jin duminta da kamshinta. Lokaci daya kuma maganganunta na zauna mishi.

****

Blocks din robar dake gabanta take shiryawa kaman katanga. Mimi dake zaune saitasa hannu tarwatsa tana wata dariya dake saka safiyya dariyar itama.

Sunkai rabin awa zaune suna wannan shiriritar. Intai dariya saitai wani gwaranci da ita kadai take son fada.

A shekara daya mimi yarinya ce mai cikakkiyar lafiya. Gashi bata da rikici sam. Indai tayi kuka to bata da lafiya. Indai da kayan wasa to bata da matsala.

Tun ranar sunan mimi safiyya tai resigning. Tagaji da aiki. Tunda fu.ad na tsare mata duk abinda take so. Tana son bama Mimi dukkan kulawar da take bukata.

Sallama safiyya taji. Sake baki tayi tana kallon fu.ad daya turo kofar ya shigo. Ware mata idanuwa yayi.

"Ki amsa sallamata ba kina mun wannan kallon ba"

"Seriously ka gudo daga kasuwa ne ko?"

Dakuna fuska yayi.

"Ni ban gudo ba. Kuma akwai su lawal a shagon. Missing ya'ta nake na zo in ganta"

Karaso wa yai falon hadi da fadin.

"Hey sweetheart. Dad is home"

Tanajin muryarshi ta ci gaba da doka hannuwanta tana tarwatsa blocks din tana dariya. Kallon safiyya yayi dake fassara kingani itama tayi kewata.

Girgiza kai safiyya tayi da murmushi a fuskarta. Fu.ad sai abarshi. Haka yake yi daga kasuwa zai gudo gida yaga mimi sannan ya koma.

Wani lokacin ma daukarta yake yi. Sai safiyya taita fada tukunna. Wasu ranakun saidai tagaji tabarshi.

Hannu yasa ya dauki mimi yana hada goshinshi da nata. Yarinyar ta saba wasan da yake mata. Ita ta soma girgiza kanta jikin nashi suna dariya tare.

"Mimi is so cute. She is so cutee"

Dariyarsu tabama safiyya dariya sosai.

"In zubo maka abinci ko?"

Ta bukata. Ya girgiza kai.

"Restaurant naje naci delicious"

Mikewa safiyya tayi tana kallon shi.

"Res....  Me? Aidaka kirani kace kar insa abinci dakai. Zaka je kaci wanda yafi shi dadi"

A kasalance ya kalleta.

"Nikam banajin yin ringima sofi. Yunwa naji and restaurant din yana kusa damu.

Mukaje muka ci abinci. Ba saiki barshi da dare muci ba?"

Sosai take kallonshi.

"Da daren ma kaje restaurant. Akwai wani a kusa damu"

Ta fadi ta na matsawa hadi da karbe mimi daga hannunshi ta juya da yarta a hannu tana barin falon.

Dariya fu.ad yake sosai. Yana so yaga safiyya na fadan nan. Kyau take kara mishi kaman ya mayar da ita cikin shi.

Saida yai mai isarshi sannan ya tashi ya bita bedroom din. Tana zaune kan gado da mimi a tsakiyar gadon. Sarai taji shigowarshi.

Taqi juyowa. Tsayawa yai wajen katon hoton nana daya ke cike da bangon dakin ya kalleta. Yana jin wata irin kewarta taban mamaki.

Hannu yasa ya shafi kumatunta a jikin hoton. Sannan yadan daga kafadarshi.

"Mumynki fushi take mun. Harda kwace Mimi daga hannu na bayan tasan saboda ita kawai na baro da kasuwa"

Shiru yai. Zai iya rantsewa yaji sautin dariyar nan ta nana dake saka shi farin ciki na daban.

"Yeah mumynki akwai rigima sosai"

Juyowa safiya tayi.

"Dadynki akwai son kai sosai. Ya fada miki kome yaimun.

Abinci fa a restaurant bayan yasan ni kaina bana iya ci saiya dawo"

Kallon hoton fu.ad yayi ya daga girarshi da ke fassara mumynki bata karantata kaman yanda kikeyi. Yasan da tana nan tunda ya bude baki zata gane wasa yake.

Sannan ya juya ya taka har inda gake. Gefen gadon ya zauna. Ya dauko mimi ya dorata kan cinyarshi sannan ya kalli safiyya da take wani basar dashi.

"Ki kalle ni sofi"

Kauda kai tayi gefe.

"Please........ Sofiii"

Ya fadi yana jan sunanta yanda yasan ba zata iya mishi gardama ba. Juyowa tayi ta sauke idanuwanta cikin nashi.

"Goodness. Kina kyau da fada"

Naushin shi tai a kafada. Ya wani dakuna fuska yana fadin.

"Ouchhh yi hakuri sofi"

Hannuwanta tasa ta matse mishi kumatu tana fadin.

"Kasan in akwai abinda na tsana baifi kaci abinci a wani waje ba"

Ture hannunta yai yana gyara ma mimi zama kan cinyarshi.

"Ki kyaleni nikam. Yunwa nakeji cikina sai ihu yake tun dazun"

Dariya tayi tana mikewa. Wani irin jiri ya dibeta ta tafi luu. Da zafin nama fu.ad ya fisgota yana zaunar da ita kan gadon.

Kanta ta dafe da hannuwa biyu tanajin yanda dakin ke wulwula mata. A rikice fu.ad ke fadin.

"Subahanallah. Sofi menene? Lafiyarki kuwa?"

Gaba daya hankalinshi ya tashi. Saida tadanji jirin ya fara tsaya sannan tace mishi.

"bakomai fa. Kawai ina jin jiriri ne wasu lokuttan"

Muryarshi babu alamun wasa a ciki yace.

"Tun yaushe?"

"Wajen sati biyu. Amman bai fara damuna ba sai kwana biyun nan"

A kufule yace.

"Sati biyu sai yanzun nake ji? Damn it sofi in wani abu ya same ki fa?"

Ganin yanda ya birkice yasata dafa hannunshi.

"Really ba wani babban abu bane ba. Kawai jiri ne. Babu inda kemun ciwo banda shi"

Ture hannunta yayi.

"Tashi mu tafi asibiti"

"Ba wani......."

Kallon dayai mata yasa ta katse maganar.

"Kaci abinci sai muje"

Muryarshi a dake ya mike da mimi a hannunshi.

"Bana jin yunwa"

Mikewa tayi tana dafa shi da fadin.

"Kayi hakuri"

Kallonta yai taga yanayin dake cikin idanuwanshi.

"Har yau inajin cewa kaman da nazo da wuri nana zata kasance tare damu.

Nasani ba tunani me kyau bane ba. Amman na kasa dainawa. What if wani abu ya sameki?

Dan Allah karki sakemun irin wannan. Da ciwo sosai"

Jikinta a sanyaye tace.

"Bazan sake ba. Please kayi hakuri"

Dan dafe kai yayi.

"Ya wuce. Dauko mayafinki muje mu dawo"

"Dakaci abincin sannan"

"Abinci can wait. Saimun dawo"

Tasan halinshi.  Tsayawa gaddama babu amfanin dazai dan haka ta wuce ta dauki hijab dinta ta saka. Suka fita.

****

Kallon jana suke su dukansu. Kallonta suke kaman kaho ne ya fito mata tsakiyar kai da maganar data gaya musu.

Kallon da suke mata ya bata dariya sosai.

"Wai menene kuke kallona haka? Nace matarka nada ciki na wata daya da sati biyu. In baku gane turancin ba"

Safiyya kallon fu.ad take zuciyarta na wani irin dokawa. Shima kallonta yake lokaci daya maganganun doctor din daya jagoranci yi mishi surgery na vasectomy suka dawo mishi.

Cikin harshen turanci yake fada ma fu.ad din cewar.

"Ko da bayan shekaru ko watanni matarka ta samu ciki karka zargeta. Ka dauka jikinka ya warkar da kanshi.

Yana faruwa ga wasu mutanen."

Hannu fu.ad yakai yana tsane gumin daya tsattsafo mishi. Zufa yake ta ko ina.

Ta bakinshi yake jan iska saboda ya daina jin shigarta na wani lokaci. Mimi ya sake gyara ma zama kan jikinshi.

Su dukansu sun kasa magana. Hawaye ke zubo ma safiyya wasu nabin wani. Tunani take wanne kyakkyawan aiki ta yi da Allah ya bata wannan kyautar.

Shi ka shi fu.ad tunanin da yake kenan.

"Oh Allah. Ina bayin da suka sake ka suka kama waninka? Hakika suna cikin bata mai muni"

Ya karasa maganar yana jin wasu hawaye masu dumi sun zubo mishi. Hannunshi safiyya ta kamo da nata duka biyun.

Ya dago dasu ya sumbace su saboda mimi dake hannunshi. Ya kasa tsaida hawayenshi. Allah Ya dube shi da Rahma ya mishi kyauta daya yanke rai da samunta.

Hakika indai kana da rai. Baka fidda rabo. Saidai Rabonka yai jinki. Inda Allah ya rubuta maka shi to saika samu.

Mimi kaman tasan farin cikin da suke. Ta kyalkyale da dariya. Kallonta sukai a tare suna murmushi though hawayen da suke zubdawa.

Doc jana kuwa gyara zama tai tana kallon su tana koyan darussa masu dama daga rayuwarsu. Da murmushi a fuskarta.

Kallon cikin safiyya fu.ad yayi ya kalli mimi. Ita kuma kallonshi take. Lokaci daya abinda su duka biyun suke tunani ya bayyana a fuskarsu.

Hannu safiyya takai da sauri ta karbi mimi tana rungumeta. Hawaye na sake zubo mata.

"No please. Ba zasuyi mana haka ba"

Yanda tai maganar yagane so take ya tabbatar mata. Sadda kanshi kasa yai da wannan sabon farin cikin daya same shi fargaba na rabuwa kusa dashi.

Mikewa yayi ya mika mata hannunshi tasa nata ciki suka juya. Jana murmushi ta sake yi dan ganin sun tafi wata duniya ta daban.

Sanda suka samu natsuwa sun nemeta.

****

Daga bedroom ya fito zee na zaune a
falo kan kafet da plantain chips a gabanta tana ci tana danne danne da wayar lukman din.

Kusa da ita ya tako ya zauna. Hannu yakai zai dibi chips din ta janye. Dakuna fuska yayi.

"Bani wayata nima. Wai meye ma amfanin wayarki? Kullum sai kin cinye mun charge"

Dariya tai tana janye wayar gefe.

"Taka tafi dadin amfani"

Kallonta yai yana daga mata gira. Dan wayarta tafi tashi tsada da komai.

"Muyi musanya to"

Makale kafada tayi.

"Ni dai ka kyaleni ina karatuna"

Kwanciya yayi yai filo da cinyarta ta ture kanshi. Ya sake komawa.

"Dee ka dagani. Duk ka mokalemun ci nya."

Dariya ta bashi sosai.

"Dan kan nawa guda nawa yake? Nafijin dadin kwanciya anan dinne kawai"

Cikinta ya kalla.

"Nifa na kagu inga ajiyata ta nuna"

Murmushi zee tayi.

"Kwanan shi nawa dazai fito? Dan ba a jikinka yake girma bako?"

Gyara kwanciyarshi yayi.

"Da kinga yanda ake laulayin ciki kuwa."

"Allah ko? Me zakayi?"

Juya kwanciyar yai yana kallon fuskarta.

"Ai ko wanka sai kinmun. In na zauna waje daya sai dai ki daukeni ki mayar wani waje in nagaji.

Ke abinci ma inba a baki ba kuka zansa. Rikici kala kala"

Jinjina kai zee take da wani murmushi a fuskarta. Mikewa lukman yai daga kan cinyarta yana kallonta muryarshi babu wasa yace.

"Wallahi wasa nake miki."

"Aifa. Ashe ni wahala nake sha. Ga yanda ya kamata ace ina yi......."

Katse mata magana yai da fadin.

"Aa wallahi. Yanda kike yin nan ma ya isheni"

Girgiza kai tayi. Zatai magana kenan sukaji sallamar su fu.ad. Da fara.a suka tarbesu.

Zee ta kawo musu ruwa da lemo. Bama su sha ba. Mimi na hannun fu.ad tana bacci. Yanayin sanyin jikinsu lukman ya kalla.

Yasan akwai damuwa a tattare dasu.

"Lafiya dai ko?"

Ya tambaya cike da kulawa. Takardar dake hannun safiyya fu.ad ya karba ya mikama lukman.

Cike da rashin fahimta ya karbi takardar ya duba. Ta asibiti ce. Sunan safiyya ne rubuce a jiki. Wani irin dokawa zuciyarshi tai ya soma dubawa babu wata nutsuwar kirki a jikinshi.

Idanuwa ya ware. Yana sake daga takardar yana dubawa. Mamaki karara a fuskarshi. Fu.ad ya kalla da ya zuba mishi idanuwa da wani irin yanayi.

Sakkowa fu.ad yai daga kan kujerar gwiwoyinshi a kasa gaban lukman. Safiyya ma sakkowa tayi hawayenta har sun soma zuba.

Kan fu.ad na kasa yace.

"Daga asibiti nan muka zo. Bamu je ko ina ba. We have to know. We need to know ko hakan zaisa ku karbeta......"

Da rashin fahimta zainab take kallon su duka ukkun. Dan taga alama ita kadaice bata fahimci meke faruwa ba. Takardar dake hannun lukman ta karba ta na dubawa.

"Please don't take her away. Please lukman wallahi......"

Kasa karasawa fu.ad yayi saboda yanda wani abu ya tsaya mishi a wuya. Ga kirjinshi na wani irin zafi.

Kallon Mimi yake dake baccinta a jikinshi. Hannunta daya rike gam da rigarshi. Wani zafi yake ji a kirjinshi kaman wuta.

Tunanin rabashi da yarinyar nan kawai ji yake zuciyarshi na neman bugawa. Wasu hawaye masu zafi suka zubo mishi.

Safiyya dake gefen fu.ad taja hijab dinta ta goge idanuwanta muryata na sarqewa tace.

"Zamu..... Zamu hakura da babyn jikina.....dan Allah kubar mana ita"

Kallon zainab lukman yayi. Muryarshi dauke da wani emotions da ya kasa tsayarwa akan komai yace mata.

"Kingan su ko zee?"

Ita har sun sakata hawaye ma. Tasa hannu ta goge su. Har ranta tana musu murnar kyautar nan da Allah yai musu.

Kuma zuciyarta na mata wani irin yawo kan kaunar da take karanta suna ma Mimi. Kaunar da ta dauka jininka ne kawai zakai ma.

Ko tsakanin fu.ad da lukman ta fahimci akwai yiwuwar bare yai maka kaunar da dan uwanka ne zai maka.

"Allah saina fada ma abbah abinda kaimun. Taya ma wannan banzan tunanin zai zo maka?

Safiyya kema ya shafa miki yarinta ko? Allah zaku sani idan na fadaku da abbah"

Dago kai fu.ad yayi ya kalle shi. Yasa hannu ya goge fuskarshi. Muryarshi a dakushe yace.

"You are not a fucking kid lukman"

Hararshi lukman yayi.

"Kasan fu.ad ai ko? To ka kalle shi zaka san na girma sosai. Marar hankali kawai.

Wallahi da ba gaban yarka bane saina kwada maka mari ko zaka dawo hankalinka"

Zainab ta fara dariya. Kamun safiyya ta dauka. Fu.ad kanshi murmushi yake.

Lukman kam ya kasa ganin abin dariya har yanzun.

"Kubarmun gida please. Ku tafi kamun ku kara batamun rai"

"Sorry......."

Fu.ad ya fadi. Sake dakuna fuska lukman yayi.

"Please...."

Kallonshi lukman yai ya ware idanuwa.

"Dan sake cewa please muji?"

Dariya fu.ad yayi.

"Fucking grow up"

Dariya sukayi a tare. Kamun in a serious murya fu.ad yace.

"Nagode. Kamun abinda ko haneef baimun shi ba lukman. Kaunarka a gareni mai girma ce.

Taya zan iya biyanka?"

Dafa kafadarshi lukman yayi.

"Ka kasance dan uwana har karshen rayuwata. Ka kasance cikin farin ciki gwargwadon iyawar ka. We are even"

Wasu hawayen fu.ad yaji sun cika mishi idanuwa. Baisan me ya same shi da kuka ba kwanakin nan. Sai dai kawai yaji suna fitowa.

"Hakika hanyoyin Ubangiji Masu Girma ne. A kanku na yarda ko asibiti ka hadiye in Allah yai niyyar baka kyauta baka isa ka kauce mata ba.

Akanku na yarda da cewa a dukkan hakuri akwai riba. A dukkan tsanani akwai sauki saidai jinkiri zai iya samuwa.

Allah ya dawwamar muku da farin ciki"

Cewar zainab da takejin wata nutsuwa ta daban. Ko da family dinta basu damu da ita ba. Ga wasu da bata hada jini dasu ba tana jinsu har cikin jininta.

A kasalance safiyya tace.

"Hmm zainab. Amin. Amman Allah ya bamu zuciyar karbar jarabawarshi shine addu.ar da muka fi bukata.

Da yawan farin ciki da yawan jarabta. Wannan shine asalin Kusancin mu da mahaliccinmu"

Kai suka jinjina cike da jin maganganunta. Ganin yanda jikin kowa yai sanyi yasa lukman cewa.

"Kunsan da nana taga fuskokin ku me zata ce? Nayi laifi ko? Uncle ya naga kowa is looking so serious?"

Yanayin muryarshi da tuna Nana yasa su dariya su dukansu.

Nana ta musu nisa amman memories din data bar musu nasa su farin ciki.

Har bakin mota su lukman suka rakasu.

****

Saida suka biya gidansu inna. Babu wata kunya fu.ad ya fadama su inna kyautar da Allah yai musu.

Addu.a sukai musu gabaki daya kamun su wuce gidansu fu.ad. Yana parking din motarshi suka fito suna
cin karo da haneef.

Gaisawa yayi da su yana tambayar ya mimi. Mika mishi ita safiyya tayi yaga bacci take yace tabarta karsu motsata ta tashi.

Wuce wa cikin gida safiyya tayi abinta. Tabarsu nan. Hugging din haneef fu.ad yayi cike da farin ciki.

Harya sake shi da mamaki a fuskar haneef. Kamun fu.ad yace.

"Allah heal me haneef. Sofi ciki gareta"

Ware idanuwa haneef yayi kamun jikinshi yai sanyi.

"Allahu Akbar. Allah kenan fu.ad. oh.  Alhamdulillah"

Sosai haneef yai murna da mamaki da kuma jinjina lamari na kaddara. Kamun suyi sallama fu.ad ya shiga cikin gidan.

Safiyya ya samu da momma a zaune. Sallama yai ko jira momma ta amsa baiba ya karasa tsakiyar falon ya zauna kasa.

Kafafuwanta ya kama da hannayenshi yana dora kanshi a cinyarta. Wai saida yazo gabanta girman abinda ya samu ya sake lillibe shi.

Hawaye ke zubo mishi. Ya rasa bakin dazai fada ma momma wannan labarin.

"Fu.ad lafiya? Subahanallah. Safiyya me ya faru?"

Sadda kanta kasa tayi. Kukan da fu.ad keyi nasa hawayenta sake zuba.

Jin yanda momma ta daga hankalinta yasa shi cikin kuka fadin.

"Momma sofi ciki take da. Zan sake haihuwa. Momma addu.arku a kanmu da albarkarku tayi tasiri."

Hamdala momma take. Addu.arta kullum bai wuce Allah ya basu rabo ba.

"Fu.ad ai abin farin ciki ne bana kuka ba"

Dagowa yai gana goge fuskarshi.

"Kukan farin cikine momma."

Murmushi tai musu. Basu jima gidan ba suka wuce.....!

****

Tsakiyar dakin suka tsaya. Mimi na hannun safiyya. Mayafinta ta cire ta ajiye. Tana kallon Mimi sannan ta kalli fu.ad.

"Allah ya jikan Nana. Zata so ganin wannan ranar"

Karasowa fu.ad yayi kusa da ita yana hade sauran space din dake tsakaninsu. Yasa hannu ya dago da habarta.

"Tana inda yafiye mata nan sau dubu. Saimu cika aikin daza mu sameta"

"Allahumma amin"

Safiyya ta fadi da murmushi.

Rikota yai ita da mimi jikinshi yana kissing goshinta.

"Alhamdulillah da rayuwarmu ta baya ta koya mana darussa da dama. Alhamdulillah da rayuwar da muka samu yanxun.

Alhamdulillah da duk tsarin da Allah yai mana nan gaba"

Rikoshi tai da dayan hannunta tana jin wata kaunarshi ta daban tana ratsa ta.

"Ina sonka sosai. Kaddarar data hadamu ta koya mana darussa da dama. Alhamdulillah"

Murmushi yayi.

"Ta kara mana imani. Alhamdulillah. Ina sonki sosai"

Ya fadi yana lumshe idanuwanshi. Wata nutsuwa na ratsa shi. Tabbas duk wanda ya Rike Allah ya yarda da Kaddara mai kyau ko marar kyau yana tare da Nasara.

*#TeamAS*

No comments:

Post a Comment